Home General Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta musanta karin kudin Man fetur

Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta musanta karin kudin Man fetur

Gwamnatin Najeriya ta musanta yin ƙarin farashin man fetur, duk kuwa da ƙaruwar farashin man a faɗin ƙasar.

Kafafen yaɗa labarai  sun ambato ƙaramin ministan albarkatun man fetur na ƙasar Timipre Sylva a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a, ta hannun mai taimaka masa kan kafofin yaɗa labarai, cewa Shugaban ƙasar bai amince da wani ƙarin sabon farashi ga man fetur ɗin ba.

A ranar Juma’ar ne dai shugaban masu gidajen mai masu zaman kansu reshen Jihar Kano Bashir Danmallam ya tabbatar wa manema labarai ƙarin farashin man fetur ɗin da kashi 8.8 cikin 100, inda ya ce sun samu umarni daga gwamnatin tarayya.

To sai dai sanarwar da ƙaramain ministan man fetur ɗin ya fitar ta ce ”babu wani dalili da shugaban ƙasar zai amince da ƙarin farashin man a daidai wannan lokaci”.

Sanarwar ta ci gaba da cewa ”gwamnati ba za ta amince da ƙarin farashin man fetur a asirce ba, ba tare da tuntuɓar masu ruwa da tsaki a fannin man fetur din ba”.

”Dan haka shugaban ƙasa bai umarci ƙungiyar dillalan man fetur da cewa su ƙara kuɗin man fetur ɗin ba”, in ji sanarwar

Haka kuma sanarwar ta ambato ministan na yin kira ga ‘yan ƙasar da su kwantar da hankulansu, su kuma zama masu bin doka, a yayin da gwamnatin ƙasar ke iya bakin ƙoƙarinta wajen wajen dawo da al’amuran rarraba man kamar yadda aka saba a baya.

Tun cikin watan Oktoban bara ne dai ake fuskantar ƙarancin man fetur a wasu sassan ƙasar, lamarin da ya haddasa sayar da man a mabambantan farashi a sassan ƙasar wadda ta fi kowacce ƙasa arzikin man fetur a nahiyar Afirka.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp