Home General Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta musanta karin kudin Man fetur

Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta musanta karin kudin Man fetur

Gwamnatin Najeriya ta musanta yin ƙarin farashin man fetur, duk kuwa da ƙaruwar farashin man a faɗin ƙasar.

Kafafen yaɗa labarai  sun ambato ƙaramin ministan albarkatun man fetur na ƙasar Timipre Sylva a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a, ta hannun mai taimaka masa kan kafofin yaɗa labarai, cewa Shugaban ƙasar bai amince da wani ƙarin sabon farashi ga man fetur ɗin ba.

A ranar Juma’ar ne dai shugaban masu gidajen mai masu zaman kansu reshen Jihar Kano Bashir Danmallam ya tabbatar wa manema labarai ƙarin farashin man fetur ɗin da kashi 8.8 cikin 100, inda ya ce sun samu umarni daga gwamnatin tarayya.

To sai dai sanarwar da ƙaramain ministan man fetur ɗin ya fitar ta ce ”babu wani dalili da shugaban ƙasar zai amince da ƙarin farashin man a daidai wannan lokaci”.

Sanarwar ta ci gaba da cewa ”gwamnati ba za ta amince da ƙarin farashin man fetur a asirce ba, ba tare da tuntuɓar masu ruwa da tsaki a fannin man fetur din ba”.

”Dan haka shugaban ƙasa bai umarci ƙungiyar dillalan man fetur da cewa su ƙara kuɗin man fetur ɗin ba”, in ji sanarwar

Haka kuma sanarwar ta ambato ministan na yin kira ga ‘yan ƙasar da su kwantar da hankulansu, su kuma zama masu bin doka, a yayin da gwamnatin ƙasar ke iya bakin ƙoƙarinta wajen wajen dawo da al’amuran rarraba man kamar yadda aka saba a baya.

Tun cikin watan Oktoban bara ne dai ake fuskantar ƙarancin man fetur a wasu sassan ƙasar, lamarin da ya haddasa sayar da man a mabambantan farashi a sassan ƙasar wadda ta fi kowacce ƙasa arzikin man fetur a nahiyar Afirka.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp