Home General NNPP tayi Alla-wadai da harin da ‘yan daba su kai gidan Muhy...

NNPP tayi Alla-wadai da harin da ‘yan daba su kai gidan Muhy Magaji

Babbar jam’iyyar adawa ta NNPP a jihar Kano ta yi Allah wadai da harin da ake zargin wasu yan jam’iyyar APC sun kai gidan Barr. Muhuyi Magaji dake Rimingado da kuma wasu yan jam’iyyar NNPP mazauna garin a daren jiya talata.
‘Yan daba da ake kyautata zaton gwamnatin APC ce ta daukI nauyinsu sun farwa al’ummar da misalin karfe 7:00 na dare bayan da tawagar yakin neman zaben jam’iyyar NNPP suka gama taronsu a garin na Rimingado .
Jam’iyyar NNPP ta jajanta wa al’ummar yankin kan lamarin da ya yi sanadin jikkatar mutane da dama da kuma barnata kadarorin al’ummar garin, Kuma NNPP ta zargin hakan wani yunkuri ne da APC ke yi na tsoratar da al’umma masu kada kuri’a a zaben dake tafe .
A cikin wata sanarwa da Sanusi Bature Dawakin Tofa, babban mai magana da yawun kwamitin yakin neman zaben NNPP na kano ya fitar, ya bayyana harin a matsayin na abun da baj dace ba, da Kuma rashin mutunta mutanen Rimingado.
Sanusi Bature ya kara da cewa babu wani matsin lamba da zai hana jam’iyyar NNPP ta dauki matakin da ya dace na cin zarafin ‘yan kasa, wanda kamata yayi jami’an gwamnati su maida hankali wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a.
“Mun yi sa’a, ‘yan sanda sun kama daya daga cikin wadanda suka kai harin, kuma wanda aka kama shi ne ya raunata guda cikin yan sandan dake aiki a Rimingado.”
Kakakin ya kuma ce, NNPP za ta tabbatar da cewa an yi adalci ga wadanda abin ya shafa tare da gurfanar da wadanda ake zargin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp