Home General NNPP tayi Alla-wadai da harin da ‘yan daba su kai gidan Muhy...

NNPP tayi Alla-wadai da harin da ‘yan daba su kai gidan Muhy Magaji

Babbar jam’iyyar adawa ta NNPP a jihar Kano ta yi Allah wadai da harin da ake zargin wasu yan jam’iyyar APC sun kai gidan Barr. Muhuyi Magaji dake Rimingado da kuma wasu yan jam’iyyar NNPP mazauna garin a daren jiya talata.
‘Yan daba da ake kyautata zaton gwamnatin APC ce ta daukI nauyinsu sun farwa al’ummar da misalin karfe 7:00 na dare bayan da tawagar yakin neman zaben jam’iyyar NNPP suka gama taronsu a garin na Rimingado .
Jam’iyyar NNPP ta jajanta wa al’ummar yankin kan lamarin da ya yi sanadin jikkatar mutane da dama da kuma barnata kadarorin al’ummar garin, Kuma NNPP ta zargin hakan wani yunkuri ne da APC ke yi na tsoratar da al’umma masu kada kuri’a a zaben dake tafe .
A cikin wata sanarwa da Sanusi Bature Dawakin Tofa, babban mai magana da yawun kwamitin yakin neman zaben NNPP na kano ya fitar, ya bayyana harin a matsayin na abun da baj dace ba, da Kuma rashin mutunta mutanen Rimingado.
Sanusi Bature ya kara da cewa babu wani matsin lamba da zai hana jam’iyyar NNPP ta dauki matakin da ya dace na cin zarafin ‘yan kasa, wanda kamata yayi jami’an gwamnati su maida hankali wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a.
“Mun yi sa’a, ‘yan sanda sun kama daya daga cikin wadanda suka kai harin, kuma wanda aka kama shi ne ya raunata guda cikin yan sandan dake aiki a Rimingado.”
Kakakin ya kuma ce, NNPP za ta tabbatar da cewa an yi adalci ga wadanda abin ya shafa tare da gurfanar da wadanda ake zargin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp