Home General NNPP tayi Alla-wadai da harin da ‘yan daba su kai gidan Muhy...

NNPP tayi Alla-wadai da harin da ‘yan daba su kai gidan Muhy Magaji

Babbar jam’iyyar adawa ta NNPP a jihar Kano ta yi Allah wadai da harin da ake zargin wasu yan jam’iyyar APC sun kai gidan Barr. Muhuyi Magaji dake Rimingado da kuma wasu yan jam’iyyar NNPP mazauna garin a daren jiya talata.
‘Yan daba da ake kyautata zaton gwamnatin APC ce ta daukI nauyinsu sun farwa al’ummar da misalin karfe 7:00 na dare bayan da tawagar yakin neman zaben jam’iyyar NNPP suka gama taronsu a garin na Rimingado .
Jam’iyyar NNPP ta jajanta wa al’ummar yankin kan lamarin da ya yi sanadin jikkatar mutane da dama da kuma barnata kadarorin al’ummar garin, Kuma NNPP ta zargin hakan wani yunkuri ne da APC ke yi na tsoratar da al’umma masu kada kuri’a a zaben dake tafe .
A cikin wata sanarwa da Sanusi Bature Dawakin Tofa, babban mai magana da yawun kwamitin yakin neman zaben NNPP na kano ya fitar, ya bayyana harin a matsayin na abun da baj dace ba, da Kuma rashin mutunta mutanen Rimingado.
Sanusi Bature ya kara da cewa babu wani matsin lamba da zai hana jam’iyyar NNPP ta dauki matakin da ya dace na cin zarafin ‘yan kasa, wanda kamata yayi jami’an gwamnati su maida hankali wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a.
“Mun yi sa’a, ‘yan sanda sun kama daya daga cikin wadanda suka kai harin, kuma wanda aka kama shi ne ya raunata guda cikin yan sandan dake aiki a Rimingado.”
Kakakin ya kuma ce, NNPP za ta tabbatar da cewa an yi adalci ga wadanda abin ya shafa tare da gurfanar da wadanda ake zargin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp