Home General ‘Yan Bindiga sun yi garkuwa da Dagaci a Jihar Kaduna

‘Yan Bindiga sun yi garkuwa da Dagaci a Jihar Kaduna

Rahotannin daga jihar kaduna na bayyana cewa ‘yan bindiga sun yi garkuwa da Chief Joshua Ahmadu dagacin
Garin Chawai dake karamar Hukumar Kauru a jihar kaduna.
Shugaban kungiyar cigaban Chawai Mista Abel Adamu ne ya tabbatar da sace dagacin a ranar Laraba.
Adamu ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun kakakin CDA yace an dauke Dagacin ne a daren talata bayan da ‘Yan bindigar suka kutsa cikin gidan sa dake Zambina.”
” ‘Yan bindigar sun shiga gidan dagacin ne da misalin karfe 9:30pm inda sukayi awon gaba da shi. A cewar Adamu.
Daga bisani Shugaban kungiyar ya bayyana takaicin sa bisa wannan aiki sannan kuma ya bayyana yadda suke fafutuka wajen ganin sun kubutar da shi ba tare da wani abu ya same shi ba.

“tuni mun sanar da masu ruwa da tsaki da jami’an tsaro wanda tuni sun fara gudanar da abin da ya dace domin kubutar da shi.
“muna kira da daukacin Al’ummar garin Tsam maza da mata dasu yi addu’ar dawowar shugaban mu cikin koshin lafiya.

Sanarwar ta kuma kalubalanci matasa dake karkashin Masarautar dasu zage dantse wajen ganin sun tabbatar da tsaro kada wannan lamari ya sake faruwa.
“ya kamata mu tsaya da kafar mu domin tabbatar da tsaro da kubuta daga matsalar rashin sa.

NAN

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp