Home General ‘Yan Bindiga sun yi garkuwa da Dagaci a Jihar Kaduna

‘Yan Bindiga sun yi garkuwa da Dagaci a Jihar Kaduna

Rahotannin daga jihar kaduna na bayyana cewa ‘yan bindiga sun yi garkuwa da Chief Joshua Ahmadu dagacin
Garin Chawai dake karamar Hukumar Kauru a jihar kaduna.
Shugaban kungiyar cigaban Chawai Mista Abel Adamu ne ya tabbatar da sace dagacin a ranar Laraba.
Adamu ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun kakakin CDA yace an dauke Dagacin ne a daren talata bayan da ‘Yan bindigar suka kutsa cikin gidan sa dake Zambina.”
” ‘Yan bindigar sun shiga gidan dagacin ne da misalin karfe 9:30pm inda sukayi awon gaba da shi. A cewar Adamu.
Daga bisani Shugaban kungiyar ya bayyana takaicin sa bisa wannan aiki sannan kuma ya bayyana yadda suke fafutuka wajen ganin sun kubutar da shi ba tare da wani abu ya same shi ba.

“tuni mun sanar da masu ruwa da tsaki da jami’an tsaro wanda tuni sun fara gudanar da abin da ya dace domin kubutar da shi.
“muna kira da daukacin Al’ummar garin Tsam maza da mata dasu yi addu’ar dawowar shugaban mu cikin koshin lafiya.

Sanarwar ta kuma kalubalanci matasa dake karkashin Masarautar dasu zage dantse wajen ganin sun tabbatar da tsaro kada wannan lamari ya sake faruwa.
“ya kamata mu tsaya da kafar mu domin tabbatar da tsaro da kubuta daga matsalar rashin sa.

NAN

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp