Home General ‘Yan Bindiga sun yi garkuwa da Dagaci a Jihar Kaduna

‘Yan Bindiga sun yi garkuwa da Dagaci a Jihar Kaduna

Rahotannin daga jihar kaduna na bayyana cewa ‘yan bindiga sun yi garkuwa da Chief Joshua Ahmadu dagacin
Garin Chawai dake karamar Hukumar Kauru a jihar kaduna.
Shugaban kungiyar cigaban Chawai Mista Abel Adamu ne ya tabbatar da sace dagacin a ranar Laraba.
Adamu ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun kakakin CDA yace an dauke Dagacin ne a daren talata bayan da ‘Yan bindigar suka kutsa cikin gidan sa dake Zambina.”
” ‘Yan bindigar sun shiga gidan dagacin ne da misalin karfe 9:30pm inda sukayi awon gaba da shi. A cewar Adamu.
Daga bisani Shugaban kungiyar ya bayyana takaicin sa bisa wannan aiki sannan kuma ya bayyana yadda suke fafutuka wajen ganin sun kubutar da shi ba tare da wani abu ya same shi ba.

“tuni mun sanar da masu ruwa da tsaki da jami’an tsaro wanda tuni sun fara gudanar da abin da ya dace domin kubutar da shi.
“muna kira da daukacin Al’ummar garin Tsam maza da mata dasu yi addu’ar dawowar shugaban mu cikin koshin lafiya.

Sanarwar ta kuma kalubalanci matasa dake karkashin Masarautar dasu zage dantse wajen ganin sun tabbatar da tsaro kada wannan lamari ya sake faruwa.
“ya kamata mu tsaya da kafar mu domin tabbatar da tsaro da kubuta daga matsalar rashin sa.

NAN

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp