Home General Jirgin kasa dauke da fasinjoji ya kauce hanya tsakanin Abuja zuwa Kaduna

Jirgin kasa dauke da fasinjoji ya kauce hanya tsakanin Abuja zuwa Kaduna

Shugaban Hukumar Jiragen kasa a Najeriya NRC Inginiya Fidet Okhiria ya tabbatar da faruwar hadarin, to sai dai ya ce suna ci gaba da bincike domin tantance dalilan faruwar lamarin ba.

Wannan hadari dai ya faru ne kasa da mako daya bayan bayan da wani jirgin daukar fasinja ya kauce wa hanyarsa a layin dogon da ya tashi daga Itakpe zuwa Warri a cikin jihar Kogi da ke tsakiyar kasar.

To sai dai wasu bayanai na nuni da cewa ga alama jirgin ya kauce wa hanyarsa ne sakamakon zagon kasa, ko dai daga masu satar kwangiri domin sayarwa ko kuma tsageranci.

Dubban mutane ne ke amfani da jirgin kasa daga Abuja zuwa Kaduna a matsayin hanyar sufuri domin zuwa yankin Arewacin Najeriya, duk da cewa watanni 9 da suka gabata, ‘yan ta’adda sun dasa bam wanda ya tarwatse a lokacin da jirgin ke wucewa dauke da fasinjoji kusan 900.

Daga bisani dai ‘yan ta’addar sun yi awun gaba da wasu fasinjojin, yayin da suka kashe wasu a lokacin harin, lamarin da ya tilasta dakatar da jigiliar jiragen kasa a wannan hanya tsawon watanni 8.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp