Home General Jirgin kasa dauke da fasinjoji ya kauce hanya tsakanin Abuja zuwa Kaduna

Jirgin kasa dauke da fasinjoji ya kauce hanya tsakanin Abuja zuwa Kaduna

Shugaban Hukumar Jiragen kasa a Najeriya NRC Inginiya Fidet Okhiria ya tabbatar da faruwar hadarin, to sai dai ya ce suna ci gaba da bincike domin tantance dalilan faruwar lamarin ba.

Wannan hadari dai ya faru ne kasa da mako daya bayan bayan da wani jirgin daukar fasinja ya kauce wa hanyarsa a layin dogon da ya tashi daga Itakpe zuwa Warri a cikin jihar Kogi da ke tsakiyar kasar.

To sai dai wasu bayanai na nuni da cewa ga alama jirgin ya kauce wa hanyarsa ne sakamakon zagon kasa, ko dai daga masu satar kwangiri domin sayarwa ko kuma tsageranci.

Dubban mutane ne ke amfani da jirgin kasa daga Abuja zuwa Kaduna a matsayin hanyar sufuri domin zuwa yankin Arewacin Najeriya, duk da cewa watanni 9 da suka gabata, ‘yan ta’adda sun dasa bam wanda ya tarwatse a lokacin da jirgin ke wucewa dauke da fasinjoji kusan 900.

Daga bisani dai ‘yan ta’addar sun yi awun gaba da wasu fasinjojin, yayin da suka kashe wasu a lokacin harin, lamarin da ya tilasta dakatar da jigiliar jiragen kasa a wannan hanya tsawon watanni 8.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp