Home General Buhari ya yabawa Ganduje bisa asibitin Masu fama da cutar daji a...

Buhari ya yabawa Ganduje bisa asibitin Masu fama da cutar daji a jihar Kano

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yabawa gwamnan jihar kano Abdullahi Umar Ganduje bisa Samar da asibitin Masu fama da cutar daji a jihar Kano dake arewa maso yammacin Nijeriya.
Buhari ya bayyana haka  ne lokacin da yake bude asibitin dake unguwar giginyu a karamar hukumar Nasarawa ta jihar kano.
Buhari yace dole a ya yabawa hangen nesa na gwamna Ganduje na samar da Asibitin Saboda yadda zai taimaka wajen magance fita waje domin neman lafiya da Kuma bunkasa tattalin arzikin Nigeria.
A nasa jawabin gwamnan jihar kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya ce an samar da Asibitin ne don rage yawan fita kasashen waje domin neman lafiya.
Yace asibitin shi ne irinsa na farko a Nigeria da Africa baki daya, Kuma zai bunkasa tattalin arzikin jihar kano da kasa baki daya.
An dai sanyawa Asibitin sunan Mai dakin gwamnan kano Farfesa Hafsat Abdullahi Ganduje.
Bayan nan Shugaba Buhari ya bude katafariyar Gadar dake Hotoro wacce aka Saka mata sunan Muhammadu Buhari, da gidajen gwamnatin tarayya dake Darmanawa da Kuma Cibiyar koyar da sana’o’i ta Aliko Dangote dake kan titin Zaria da dai sauran su.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp