Home General Jirgin Kasan Kaduna zuwa Abuja zai dawo aiki ranar talata

Jirgin Kasan Kaduna zuwa Abuja zai dawo aiki ranar talata

Hukumar Zirga-Zirgar Jiragen Kasa ta Najeriya (NRC) ta sanar da dawowar aiki jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna wanda aka dakatar sakamakon hatsari da ya yi a tashar Kubwa a makon da ya gabata, ranar Juma’a 27 ga watan Janairu, 2023.
NRC a cikin wata sanarwa, ta ambaci Daraktan Ayyuka, Injiniya Niyi Ali, na cewa jirgin zai dawo aiki a ranar Talata 31 ga Janairu 2023.
Jadawalin jirgin da aka fitar ya nuna jirgin farko daga Kaduna zuwa Abuja zai tashi da karfe 7 na safe yayin da jirgin farko daga Abuja zuwa Kaduna zai tashi da karfe 10 na safe.
Jirgi na biyu daga Kaduna zai tashi da karfe 1:00 na rana, yayin da jirgin Abuja zuwa Kaduna zai tashi da karfe 4 na yamma.
Sai dai a ranar Laraba jirgin kasa daya ne zai tashi daga Kaduna zuwa Abuja da misalin karfe 7 na safe sai kuma wanda zai tashi daga Abuja zuwa Kaduna da misalin karfe 4 na yamma.
“Muna nadamar duk wata matsala da fasinjojinmu masu suka fuskanta sakamakon matsala da jirgi ya samu ya samu.”

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fiye da Kashi 60 na 'Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara - IMFGwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasartaƳan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a Kano
X whatsapp