Home General ‘Yan sanda a kano sun kubutar da yaran da akayi garkuwa dasu...

‘Yan sanda a kano sun kubutar da yaran da akayi garkuwa dasu a jihar

Rundunar ‘Yan Sandan Kano ta kama wasu matasa guda biyu da ake zargi da garkuwa da wasu Yara guda 2 har suka nemi a tura musu Naira Miliyan 20 a matsayin kudin Fansa.

Cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar yan sandan jihar kano DSP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar, yace rundunar ta yi nasarar kama matasan ne lokacin da suka aikowa da Iyayen yaran da suka sace da wasika mai dauke da lambar wayarsu da Kuma account number domin tura musu kuɗin fansa.

Yace Matasa Masu suna Nura Auwal Mai shekaru 22 mazaunin Rijiyar lemo da abokin sa Abubakar Lawan mai shekaru 22 mazaunin Bachirawa a kano sun bukaci a iyayen yaran da su basu Naira Miliyan 20 a matsayin kuɗin fansa, yayin da daga bisani suka Amince zasu karbi Naira Miliyan 4 kafin su sake su.

Kiyawa yace tuni wadanda ake zargi suka amsa laifin da ake zargin su da aikatawa, kuma kwamishinan ‘yan sandan jihar kano CP Mamman Dauda ya bada umarnin fadada bincike da Kuma gurfanar da su a gaban kotu domin yanke musu hukunci daidai da laifin su.

Kiyawa yace tuni aka ceto yaran wadanda kowannen su bai wuce shekaru 3 zuwa 4 a Wani kango Inda aka ajiye su, bayan sun karbi korafi daga wani Auwal Sale tun a ranar 26 ga watan Janairu 2023.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp