Home General ‘Yan sanda a kano sun kubutar da yaran da akayi garkuwa dasu...

‘Yan sanda a kano sun kubutar da yaran da akayi garkuwa dasu a jihar

Rundunar ‘Yan Sandan Kano ta kama wasu matasa guda biyu da ake zargi da garkuwa da wasu Yara guda 2 har suka nemi a tura musu Naira Miliyan 20 a matsayin kudin Fansa.

Cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar yan sandan jihar kano DSP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar, yace rundunar ta yi nasarar kama matasan ne lokacin da suka aikowa da Iyayen yaran da suka sace da wasika mai dauke da lambar wayarsu da Kuma account number domin tura musu kuɗin fansa.

Yace Matasa Masu suna Nura Auwal Mai shekaru 22 mazaunin Rijiyar lemo da abokin sa Abubakar Lawan mai shekaru 22 mazaunin Bachirawa a kano sun bukaci a iyayen yaran da su basu Naira Miliyan 20 a matsayin kuɗin fansa, yayin da daga bisani suka Amince zasu karbi Naira Miliyan 4 kafin su sake su.

Kiyawa yace tuni wadanda ake zargi suka amsa laifin da ake zargin su da aikatawa, kuma kwamishinan ‘yan sandan jihar kano CP Mamman Dauda ya bada umarnin fadada bincike da Kuma gurfanar da su a gaban kotu domin yanke musu hukunci daidai da laifin su.

Kiyawa yace tuni aka ceto yaran wadanda kowannen su bai wuce shekaru 3 zuwa 4 a Wani kango Inda aka ajiye su, bayan sun karbi korafi daga wani Auwal Sale tun a ranar 26 ga watan Janairu 2023.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp