Home General CBN yace bankuna zasu cigaba da karbar tsuffin kudi bayan wa’adi ya...

CBN yace bankuna zasu cigaba da karbar tsuffin kudi bayan wa’adi ya kare

Gwamnan Babban Bankin Najeriya Godwin Emefiele ya ce bankunan ƙasar za su ci gaba da karɓar tsoffin takardun kuɗi daga hannun kwastomominsu har zuwa bayan wa’adin 10 ga watan Fabrairu, lokacin da za a daina amfani da tsoffin takardun kuɗin a ƙasar

Mista Emefiele ya bayyana hakan ne a lokacin da ya hallara a gaban kwamitin wucin-gadi kan sauya fasalin kuɗin ƙasar na majalisar wakilan ƙasar.

To sai dai gwamnan Babban Bankin bai bayyana lokacin da bankunan za su daina karɓar tsoffin takardun kuɗin ba.

Tun da farko dai kakakin Majalisar Wakilan ƙasar Femi Gbajabiamila, ya zargi gwamnan Babban Bankin da saɓa wa sashe na 20 na dokar CBN wadda a cewarsa ta wajabta wa bankunan ci gaba da karɓar tsoffin kudin har zuwa bayan wa’adin da Babban Bankin ya saka.

Yayin da yake jawabi a gaban kwamitin Emefiele, ya ce ya yarda da ‘yan majalisar game da sashe na 20 na dokar CBN.

”Sashe na 20 na cewa bayan cikar wa’adi za a daina amfani da tsoffin takardun kuɗi, to amma an wajabta wa bankuna karɓar ƙuɗaɗen. Dan haka ina tare da majalisa a kan haka”, in ji Emefiele.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp