Home General Likitocin Nijeriya sun fasa Yajin Aiki

Likitocin Nijeriya sun fasa Yajin Aiki

Ƙungiya Likitoci Masu Neman Ƙwarewa ta Najeriya ta soke yajin aikin da ta shirya gudanarwa a faɗin ƙasar.

Matakin na zuwa ne bayan ganawar da kwamitin zartarwa na ƙungiyar ya gudanar a birnin Uyo na jihar Akwa Ibom, inda ƙungiyar ta sake duba batun.

A cikin watan Janairu ne dai ƙungiyar ta yi barazanar tafiya yajin aiki a fadin ƙasar saboda kasa biya mata buƙatunta da gwamnati ta yi.

Likitocin dai na buƙatar a sake duba tare da inganta kuɗaɗen alawus ɗin horaswa da ake ba su, yayin da suke kuka da rashin biyansu wasu alawus-alawus, da rashin biyan wasu daga cikin mambobinsu da sabon tsarin albashi da ƙasar ta amince da shi.

Rahotonni sun ce a ƙarshen ganawar majalisar zartarwar ƙungiyar, likitocin sun yaba wa gwamnatin tarayya game da sakin sabuwar sanarwar biyan kuɗaɗen alawus-alawus na horaswa ga likitocin.

Haka kuma likitocin sun nemi gwamnatin tarayyar da ta biya wasu daga cikin mambobinta da ke bin gwamnatin bashin kuɗaden alawus-alawus.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp