Home General Hukumar ICPC ta kama Manajan Banki da Boye Sabon Kudi

Hukumar ICPC ta kama Manajan Banki da Boye Sabon Kudi

Hukumar yaƙi da laifukan cin hanci da rashawa a Najeriya, ICPC, ta kama manajan ayyuka na reshen bankin FCMB a Jihar Osun saboda zargin ɓoye sababbin takardun naira.

ICPC ta ce ta gano an zuba kuɗi a cikin na’urorin ATM na bankin amma a ɗaɗɗaure ta yadda ba za su iya fita ba idan mutane suka je cira, inda ta yi gargaɗi da a gyara.

“Sai dai da tawagar ta sake kai ziyarar duba a rana ta biyu, sai ta tarar ɗaya daga cikin ATM ɗin na ɗauke da ɗaurarrun kuɗin,” a cewar sanarwar da ICPC ta wallafa a shafukan zumunta.

Bisa wannan dalilin ne kuma jami’an hukumar suka tafi da manajan mai kula da ayyuka, wanda ba ta bayyana sunansa ba, na reshehn bankin na FCMB.

Haka nan, ICPC ta kama wata manajar bankin a Abuja “saboda ƙin saka kuɗi a ATM da gangan ko kuma sabo da mugunta duk da cewa akwai kuɗin,” in ji hukumar.

Jami’an tsaro da suka haɗa da na ‘yan sanda da EFCC na ci gaba da bin sawun bankuna da ɗaiɗaikun mutane don yaƙi da masu ɓoyewa da sayarwa da kuma yaɗa takardun jabu na sababbin kuɗin.

A gefe guda kuma, ‘yan Najeriya na ci gaba da kokawa kan ƙarancin kuɗin, inda suke shafe awanni a kan dogayen layuka don cirar su a na’urorin ATM.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp