Home General Hukumar NDLEA ta Kama Mai Juna Biyu Kan Kokarin Safarar Miyagun Kwayoyi

Hukumar NDLEA ta Kama Mai Juna Biyu Kan Kokarin Safarar Miyagun Kwayoyi

Wata mata mai dauke da juna biyu ta fada komar NDLEA bayan da tayi kokarin safarar miyagun kwayoyi.

Matar wanda ta kunshe wiwi a cikin kananan rediyo guda biyu, tayi nufin aika kayan Dubai kafin ta shiga hannu.

Jami’an NDLEA na ci gaba da yunkuri wajen dakile sha da fataucin miyagun kwayoyi kamar yadda kakin su na Lagos ya bayyana.

Legas – Jami’an hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi (NDLEA) da ke sansanin fita da kaya ta NAHCO shiyyar filin tashi da saukar jiragen sama na Murtala Muhammad, da ke Ikeja, Lagos, sun kama wata mata mai juna biyu, Mrs Sylvester Gloria Onome, ranar Litin, 30 ga watan Janairu, 2023, saboda samun ta da miyagun kwayoyi.

Mai magana da yawun hukumar, Femi Babafemi, ranar Lahadi a Abuja ya ce an kama matar da giram 800 na wiwi da aka boye a cikin kananan rediyo da za a tura Dubai, Hadaddiyar Daular Larabawa, rahoton Vanguard.

Duk a ranar, Hukumar NDLEA ta kuma dakatar da wasu kayan da aka tura jamhuriyyar Congo, Kinshasa, dauke da kwalabe 111 da mayukan shafawa da aka boye kilo 24.50 na ephedrine, wani sinadari da ake amfani da shi wajen hada methamphetamine

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp