Home General Kotun Koli ta Tabbatar da Ahmad Lawan a Matsayin ‘Dan Takarar Sanata...

Kotun Koli ta Tabbatar da Ahmad Lawan a Matsayin ‘Dan Takarar Sanata na Yankin Yobe

Rahotannin daga Nijeriya na bayyana cewa Kotun koli ta tabbatar da Ahmad Lawan, shugaban majalisar dattawan Najeriya matsayin ‘dan takarar sanata na yankin Yobe ta arewa a karkashin jam’iyyar APc a zabe mai zuwa,

A hukunci mafi rinjaye da aka yanke a ranar Litinin, kotun kolin ta soke hukuncin kotun daukaka kara wacce ta ayyana Bashir Machina matsayin ‘dan takarar kujerar sanatan Yobe ta arewa a APC.

Jam’iyyar APC na ƙalubalantar Bashir Machina a matsayin ɗan takararta na kujerar sanatan Yobe ta Arewa.

Jam’iyyar ta kafe cewa shugaban majalisar dattawan ƙasar Sanata Ahmad Lawan ne halastaccen ɗan takararta a babban zaɓen ƙasar da ke tafe.

A zaman sauraron ƙarar da ya gabata, lauyan jam’iyyar Sepiribo Peters ya ce zaɓen fitar da gwanin da ya bai wa machina nasara, ya saɓa wa dokar zaɓe ta 2022.

Peters ya ce ba jam’iyyar ce ta naɗa Danjuma Manga a matsayin jami’in da ya jagoranci zaɓen fitar da gwanin ba.

Ya shaida wa kotun cewa jam’iyyar APC ta soke zaɓen fitar da gwanin sakamakon matsalolin da aka samu a lokacin gudanar da zaɓen.

Ya kuma ce kwamitin gudanarwar jam’iyyar ya sake shirya wani zaɓen fitar da gwanin ranar 9 ga watan Yuni, inda kuma Ahmad Lawan ya yi nasara.

To sai dai lauyan Bashir Machina Sarafa Yusuf ya ce yana fatan Kotun Ƙolin za ta yi watsi da ƙarar sakamakon rashin ƙwararan hujjoji, kasancewar Shugaban Majalisar Dattawan bai ƙalubalanci hukuncin da kotunan baya suka yi ba.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp