Home General Buhari ya Amince da kafa Kwamitin shirye-shiryen Mika mulki

Buhari ya Amince da kafa Kwamitin shirye-shiryen Mika mulki

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya amince da nadin kwamitin shirye-shiryen mika mulki na ofishin shugaban kasa, wanda zai gabatar da dukkan ayyukan shirin mika mulki ga sabuwar gwamnatin da za ta gaji wannan bayan zaben 2023.

Wannan na cikin wata sanarwa da Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya ya fitar da sa hannun Willie Bassey wanda shi ne daraktan yada labarai a ofishin.

Ga mambobin kwamitin:

1. Sakataren Gwamantin Tarayya – Shugaban kwamitin 2. Shugaban Ma’aikatan Gwamnatin Tarayya 3. Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya kuma babban sakatare a ma’aikatar shari’a 4. 

Manyan sakatarori daga wadannan ma’aikatun gwamnatin tarayya:

  • Tsaro
  • Harkokin Cikin Gida
  • Kudi da Kasafi da Tsare-tsare
  • Harkokin Waje
  • Yada Labarai da Al’adu
  • Babban Birnin Tarayya (FCTA)
  • Ayyuka na Musamman
  • Ofishin Shugaban Kasa, karkashin Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya
  • Ofishin Ayyukan Yau da Kullum karkashin Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya
  • Ofishin kula da Tattalin Arziki da na Siyasa, karkashin Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya
  • Fadar Shugaban Kasa

5. Ofishin Mai ba Shugaban Kasa Shawara kan Tsaro

6. Hafsan Hafsoshin Sojojin Najeriya

7. Sufeto-Janar na ‘Yan Sandan Najeriya

8. Babban Daraktan Hukumar Tsaro ta NIA

9. Babban Daraktan Hukumar Tsaro ta Farin Kaya, DSS

10. Babban Akawun Kotun Kolin Najeriya

11. Wakilai biyu da zababben Shugaban Kasa zai nada

Sakataren Gwamnatin Tarayya ne zai kaddamar da wannan kwamitin ranar Talata 14 ga watan Fabrairun 2023 da karfe 12 na rana a ofishin Sakataren Gwamantin Tarayya.

Baya ga wannan, Sanarwar ta ce Shugaba Buhari ya sanya hannu kan wata dokar shugaban kasa mai lamba 14 ta 2023 kan Gudarwa da Tafiyar da Ayyukan Kwamitin Mika Mulki na Mukamin Shugaban Kasa.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp