Home General Buhari ya Amince da kafa Kwamitin shirye-shiryen Mika mulki

Buhari ya Amince da kafa Kwamitin shirye-shiryen Mika mulki

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya amince da nadin kwamitin shirye-shiryen mika mulki na ofishin shugaban kasa, wanda zai gabatar da dukkan ayyukan shirin mika mulki ga sabuwar gwamnatin da za ta gaji wannan bayan zaben 2023.

Wannan na cikin wata sanarwa da Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya ya fitar da sa hannun Willie Bassey wanda shi ne daraktan yada labarai a ofishin.

Ga mambobin kwamitin:

1. Sakataren Gwamantin Tarayya – Shugaban kwamitin 2. Shugaban Ma’aikatan Gwamnatin Tarayya 3. Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya kuma babban sakatare a ma’aikatar shari’a 4. 

Manyan sakatarori daga wadannan ma’aikatun gwamnatin tarayya:

  • Tsaro
  • Harkokin Cikin Gida
  • Kudi da Kasafi da Tsare-tsare
  • Harkokin Waje
  • Yada Labarai da Al’adu
  • Babban Birnin Tarayya (FCTA)
  • Ayyuka na Musamman
  • Ofishin Shugaban Kasa, karkashin Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya
  • Ofishin Ayyukan Yau da Kullum karkashin Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya
  • Ofishin kula da Tattalin Arziki da na Siyasa, karkashin Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya
  • Fadar Shugaban Kasa

5. Ofishin Mai ba Shugaban Kasa Shawara kan Tsaro

6. Hafsan Hafsoshin Sojojin Najeriya

7. Sufeto-Janar na ‘Yan Sandan Najeriya

8. Babban Daraktan Hukumar Tsaro ta NIA

9. Babban Daraktan Hukumar Tsaro ta Farin Kaya, DSS

10. Babban Akawun Kotun Kolin Najeriya

11. Wakilai biyu da zababben Shugaban Kasa zai nada

Sakataren Gwamnatin Tarayya ne zai kaddamar da wannan kwamitin ranar Talata 14 ga watan Fabrairun 2023 da karfe 12 na rana a ofishin Sakataren Gwamantin Tarayya.

Baya ga wannan, Sanarwar ta ce Shugaba Buhari ya sanya hannu kan wata dokar shugaban kasa mai lamba 14 ta 2023 kan Gudarwa da Tafiyar da Ayyukan Kwamitin Mika Mulki na Mukamin Shugaban Kasa.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp