Home General Buhari na Jagorantar taron Majalisar Kolin kasar

Buhari na Jagorantar taron Majalisar Kolin kasar

Shugaba Buhari na jagorantar taron Majalisar Koli ta Kasa domin tattauna batutuwan da ke ci wa Najeriya tuwo a kwarya.
A na sa ran taron Majalisar da ke gudana a Fadar Shugaban Kasa zai tattauna kan matsalar mai, sauyin kudi, karancin takardun Naira da kuma sha’anin tsaro gabanin babban zabe da za a yi nan da mako biyu.
Taron ya samu halartar tsoffin shugabannin kasa irin su, Abdulsalami Abubakar, Goodluck Jonathan, Olusegun Obasanjo, da kuma Yakubu Gowon da gwamnoni da kuma Shugabannin Majalisar Dokoki ta Kasa.
Majalisar Koli ta Kasa wani bangare ne Gwamnatin Najeriya da ke ba da shawarwari kan tsare-tsaren gwamnati a bangaren zartaswa.
Mahalarta zaman na ranar Juma’a sun hada da Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN), Shugaban Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) da Shugaban ’Yan Sandan Najeriya.
Haka kuma taron ya sami halartar Mataimakin Shugaban Kasa, Yemi Osinbajo, Sakataren Gwamnatin Tarayya, Shugabar Ma’aikatan Gwamnatin Tarayya da sauransu.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp