Home General Kotun Koli ta Gargadi ‘yan Nijeriya

Kotun Koli ta Gargadi ‘yan Nijeriya

Kotun Ƙolin Najeriya ta gargaɗi masu sukarta game da hukuncin da ta yanke da ya bai wa shugaban majalisar dattawan ƙasar Sanata Ahmada Lawan da Sanata Godswill Akpabio, nasara a matsayin halastattun ‘yan takarar sanata a jam’iyyar APC.

Kotun Ƙolin dai ta umarci hukumar zaɓen ƙasar INEC da ta amince da sunayen sanatocin biyu a matsayin ‘yan takarar kujerun sanata a jam’iyyar APC mai mulkin ƙasar a babban zaɓen ƙasar da ke tafe ranar 25 ga watan Fabrairun da muke ciki.

Tun bayan wannan hukunci ne dai mutane ke cigaba da sukar kotun da ɓangaren shari’ar ƙasar, ciki har da fitaccen marubucin nan Farfesa Faroq Kperogi, ɗan Najeriya mazaunin Amurka.

A wata sanarwa da Kotun Ƙolin ƙasar ta fitar da hannun daraktan yaɗa labaranta Dakta Festus Akande ta gargaɗi masu sukar kotun da su guji aikata hakan.

Kotun ta jadadda cewa ”Mu ba ‘yan siyasa ba ne, kuma ba za mu zama ‘yan siyasa ba, dan haka bai kamata a ɗauke mu a wannan matsayi ba. Babu ra’ayin wani mutum da zai fi ra’ayin kowa. Najeriya gaba take da kowa- da-kowa, dan haka waɗannan kalamai sun isa haka”.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp