Home General Gwamnatin jihar Katsina ta kafa kwamitin Binciken musabbabin kisan ‘yan Banga a...

Gwamnatin jihar Katsina ta kafa kwamitin Binciken musabbabin kisan ‘yan Banga a jihar

Gwamnan jihar Katsina da ke arewa maso yamacin Najeriya Aminu Bello Masari ya kafa kwamiti mai mambobi 13 da zai gudanar da bincike kan kisan ‘yan sa kai sama da 100 da aka yi a wasu garuruwan ƙananan hukumomin Kankara da Bakori a jihar.

A wata sanarwa da daraktan yaɗa labaran gwamnan Al-amin Isa, ya aike wa manema labarai, ya ce ana sa ran kwamitin ƙarkashin jagorancin Hon. Justice A.B. Abdullahi, zai gudanar da bincike domin gano abun da ya haddasa kashe-kashen a waɗannan garuruwa.

Sauran ayyukan da ake sa ran kamitin zai gudanar sun haɗa da yin bincike domin gano adadin rayuka da dukiyoyin da ka rasa a lokacin kashe-kashen.

Tare da gano yawan mutanen da harin ya shafa sannan da gano ƙungiyoyi ko mutanen da ke da suka aikata ko suke da hannu wajen wannan aika-aika.

Sanarwar ta ƙara da cewa gwamnati na duba yiyuwar tallafa wa waɗanda lamarin ya rusta da su tare da iyalan mamatan, da bayar da shawarar ɗaukar matakan kare kai da bai saɓa wa doka ba, tare da ɗaukar matakai domin kare aukuwar makamancin wannan hari a nan gaba a jihar.

A makon da ya gabata ne dai rahotonni suka ce ‘yan bindiga sun yi wa wasu ‘yan sakai waɗanda ke ƙoƙarin ƙwato wasu shanun sata, kwanton ɓauna tare da kashe sama da 100 a wasu garuruwa a ƙananan hukumomin Kankara da Bakori a jihar.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp