Home General Rundunar sojojin Najeriya ta ce ba za ta lamunci labaran boge da...

Rundunar sojojin Najeriya ta ce ba za ta lamunci labaran boge da ake yaɗawa da sunan jami’anta ba

Rundunar sojojin Najeriya ta ce ba za ta lamunci labaran boge da ake yaɗawa da sunan jami’anta ba a shafukan sada zumunta.

Wannan na matsayin wani martani da ta mayar kan wasu rubuce-rubuce da ke yawo a shafukan sada zumunta, ta ce mutanen da ke kokarin haifar da ruɗani ke amfani da sunanta.

Babban Jami’in sadarwa na kasa a rundunar, Brigediya Janar Tukur Gusau, ya ce tuni sun kaddamar da bincike domin hukunta wadanda suka kirkiri wannan labari.

An dai rinƙa yawo da wasu bayanai kan rundunar da ke cewa, wasu daga cikin manyan jami’anta sun gana da daya daga cikin ‘yan takarar shugaban kasa domin kawo rudani kan zaben da ake shirin gudanarwa nan da kwanaki goma sha uku masu zuwa.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp