Home General Rundunar sojojin Najeriya ta ce ba za ta lamunci labaran boge da...

Rundunar sojojin Najeriya ta ce ba za ta lamunci labaran boge da ake yaɗawa da sunan jami’anta ba

Rundunar sojojin Najeriya ta ce ba za ta lamunci labaran boge da ake yaɗawa da sunan jami’anta ba a shafukan sada zumunta.

Wannan na matsayin wani martani da ta mayar kan wasu rubuce-rubuce da ke yawo a shafukan sada zumunta, ta ce mutanen da ke kokarin haifar da ruɗani ke amfani da sunanta.

Babban Jami’in sadarwa na kasa a rundunar, Brigediya Janar Tukur Gusau, ya ce tuni sun kaddamar da bincike domin hukunta wadanda suka kirkiri wannan labari.

An dai rinƙa yawo da wasu bayanai kan rundunar da ke cewa, wasu daga cikin manyan jami’anta sun gana da daya daga cikin ‘yan takarar shugaban kasa domin kawo rudani kan zaben da ake shirin gudanarwa nan da kwanaki goma sha uku masu zuwa.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp