Home General A karo na 3 Buhari ya sake ganawa da Emefiele,

A karo na 3 Buhari ya sake ganawa da Emefiele,

Shugaba Nijeriya Muhammadu Buhari ya yi wata ganawar sirri da Gwamnan Babban Bankin kasar (CBN) Godwin Emefiele a fadarsa da ke Abuja.

Wannan shi ne karo na uku da gwamnan yake ganawa da shugaban tun bayan matsalar karancin takardar kudin kasar na naira da ta bullo a sakamakon sauyin wasu daga cikin manyan takardun kudin na 200 da 500 da kuma 1,000 da Babban Bankin ya yi.

Bayan wannan ganawar tasu ta uku a Aso Villa, Emefiele, ya ki cewa uffan ga manema labarai lokacin da ya fito.

Bugu da kari babu wata sanarwa daga fadar ko wani jami’i na gwamnati da ya bayyana dalilin ziyarar gwamnan bankin zuwa fadar shugaban kasar.

Sai dai duk da haka ana ganin ba za ta rasa nasaba da halin da kasar ke ciki ba na karancin takardun na naira da abin da wahalhalun da al’ummar kasar suka samu kansu a ciki a dalilin canjin.

Ko a ranar laraba da ta gabata shugaban kasar ya gana da gwamnan bankin bayan Kotun Kolin kasar ta dakatar da wa’adin da bankin ya sanya na daina karbar tsofaffin kudin daga ranar 10 ga watan Fabarairu.

Har sai Kotun ta yanke hukunci ranar Laraba da ke tafe, a kan karar da gwamnonin jihohi uku – na Kaduna da Kwara da kuma Zamfara suka shigar a kan batun canjin kudin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp