Home General Gwamnatin tarayyar Najeriya ta bayar da umarnin rufe kwalejojin fasaha a faɗin...

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta bayar da umarnin rufe kwalejojin fasaha a faɗin ƙasar

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta bayar da umarnin rufe kwalejojin fasaha a faɗin ƙasar gabanin babban zaɓen ƙasar da ke tafe ranar 25 ga watan Fabrairu da 11 ga watan Maris da ke tafe.

Ministan Ilimin ƙasar Adamu Adamu ne ya sanar da haka cikin wata wasiƙa da jami’in ma’aikatar I.O Folorunsho ya sanya wa hannu, tare da aike wa babban sakataren hukumar kula da kwalejojin fasaha na ƙasa (NBTE) Idris Bugaje.

Ministan ya umarci shugabannin makarantun duka kwalejojin fasaha cewa a tsadar da karatu daga 22 ga watan Fabrairu zuwa 14 ga watan Maris.

Wasiƙar ta ci gaba da cewa ”Sakamakon fargabar da ake da ita kan tsaron tsaron malamai da ɗalibai da kadarorin makarantunmu, Ministan Ilimi Adamu Adamu bayan tuntuɓa mai zurfi da hukumomin tsaro, ya bayar da umarnin rufe duka makarantun fasahar”

”Dan haka za a rufe makarntun daga ranar Laraba 22 ga watan Fabrairu zuwa 14 ga watan Maris 2023,”

A makon da ya gabata ne dai Hukumar Kula da Jami’o’i ta Najeriya ta bayar umarnin a rufe dukkanin jami’o’in ƙasar tsawon lokacin da za a gudanar da babban zaɓen ƙasar na 2023.

A wata sanarwar mai ɗauke da sa hannun mataimakin shugaban hukumar, mai kula da harkar gudanarwa, Chris J. Maiyaki, ya ce za a rufe jami’o’in ne domin kare lafiyar ma’aikata, da ɗalibai a tsawon lokacin zaɓen.

Bayanin ya ce umurnin ya fito ne daga ministan ilimi na Najeriyar, Adamu Adamu, inda aka umurci dukkanin shugabannin jami’o’i su rufe daga 22 ga watan Fabrairu zuwa 14 ga watan Maris.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp