Home General Mutane 38 sun Mutu sakamakon cutar mashako ta (diphtheria) a jihar Kano

Mutane 38 sun Mutu sakamakon cutar mashako ta (diphtheria) a jihar Kano

Cibiyar yaki da cututtuka ta najeriya ta tabbatar da cewa mutum 216 ne cutar mashako (diphtheria) ta kama a jihohin Kano da Yobe da Lagos da kuma Osun.

Sannan kuma zuwa yanzu kamar yadda bayanan hukumar suka nuna cutar ta kashe mutum 40 a jihohin Kano da Lagos.

Daga cikin mutanen da suka rasu Kano tana da 38 yayin da Lagos take da biyu, in ji hukumar.

Haka kuma hukumar ta ce mutanen da suka kamu da rashin lafiya wadanda ake ganin ko cutar ce suma ta kama su yanzu sun kai 523 a jihohi biyar.

Jihohin kuwa su ne Kano da Yobe da Katsina da Lagos da kuma Osun.

Shugaban kwamitin kwararru da ke yaki da cutar ta mashako a hukumar ta NCDC, Dr Bola Lawal, shi ne ya gabatar da wadannan bayanai a wani taro ta intanet a jiya Litinin.

Dr Lawal ya ce hukumar ta tashi tsaye wajen taimaka wa kwararrun da ke aikin yaki da cutar a jihohin da ta bayyana na Kano da Katsina da Yobe da Lagos da kuma Osun.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp