Home General INEC ta sake Matsaya kan ajiye muhimman kayan zabe a CBN

INEC ta sake Matsaya kan ajiye muhimman kayan zabe a CBN

Hukumar zaben Najeriya, INEC, ta ce za ta adana muhimman kayan zaben 2023 a Babban Bankin kasar, bayan da a baya ta ce ba za ta yi hakan ba.

Idan dai ba a manta ba a 2022 sakamakon damuwa da jama’a da kungiyoyi suka nuna da kuma matsin lamba da aka yi wa hukumar ta INEC, kan adana kayan a CBN, bayan da Gwamnan bankin Godwin Emefiele ya nuna sha’awarsa ta yin takarar shiugabancin kasar, hukumar ta nuna cewa ba za ta ajiye kayan a can ba.

Shugaban hukumar zaben Farfesa Mahmood Yakubu, a ranar 4 ga watan Yuni 2022, ya ce ba za a kai muhimman kayan zaben CBN ba.

A ranar Talata ne Kwamishinan yada labarai da wayar da kan masu zabe na hukumar ta INEC Festus Okoye ya bayyana cewa wasu daga cikin muhimman kayan zaben suna Babban Bankin, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Okoye ya ce yuni hukumar ta samar tare da kai muhimman kayan zaben kamar su takardar rubuta sakamako da takardar zabe kuma ta adana su a bankin inda daga can za ta kai su ofisoshin INEC da ke kananan hukumomin kasar.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp