Home General INEC ta sake Matsaya kan ajiye muhimman kayan zabe a CBN

INEC ta sake Matsaya kan ajiye muhimman kayan zabe a CBN

Hukumar zaben Najeriya, INEC, ta ce za ta adana muhimman kayan zaben 2023 a Babban Bankin kasar, bayan da a baya ta ce ba za ta yi hakan ba.

Idan dai ba a manta ba a 2022 sakamakon damuwa da jama’a da kungiyoyi suka nuna da kuma matsin lamba da aka yi wa hukumar ta INEC, kan adana kayan a CBN, bayan da Gwamnan bankin Godwin Emefiele ya nuna sha’awarsa ta yin takarar shiugabancin kasar, hukumar ta nuna cewa ba za ta ajiye kayan a can ba.

Shugaban hukumar zaben Farfesa Mahmood Yakubu, a ranar 4 ga watan Yuni 2022, ya ce ba za a kai muhimman kayan zaben CBN ba.

A ranar Talata ne Kwamishinan yada labarai da wayar da kan masu zabe na hukumar ta INEC Festus Okoye ya bayyana cewa wasu daga cikin muhimman kayan zaben suna Babban Bankin, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Okoye ya ce yuni hukumar ta samar tare da kai muhimman kayan zaben kamar su takardar rubuta sakamako da takardar zabe kuma ta adana su a bankin inda daga can za ta kai su ofisoshin INEC da ke kananan hukumomin kasar.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp