Home General Festus Keyamo ya yaba da jajircewar gwamnonin jam’iyyar APC kan sauyin takardun...

Festus Keyamo ya yaba da jajircewar gwamnonin jam’iyyar APC kan sauyin takardun kudi.

Karamin Ministan Kwadago da aiki Festus Keyamo ya yaba da jajircewar gwamnonin jam’iyyar APC da suka yi adawa da gwamnatin Muhammadu Buhari a kotun koli. Festus Keyamo, babban lauyan Najeriya, ya ce ta hanyar ayyukansu, gwamnonin APC suna “yaki ne da sunan talakawa, suna fafutukar ganin jama’a su samu taimako” a kan manufofin gwamnatin.

“Duk gwamnan da ya je kotu yana gwagwarmayar talakawa, yana fafutukar ganin jama’a su samu tallafi, dukkansu gwamnonin APC ne,”kalaman Minista  Keyamo.

A makon da ya gabata ne gwamnoni uku karkashin jam’iyyar APC, Kaduna, Kogi da Zamfara suka maka gwamnatin tarayya karkashin jam’iyyar APC a kotun koli, inda suka bukaci a sauya wa’adin da aka sanya na amfani da tsofaffin takardun kudi na naira. Babban bankin Najeriya ya sanya ranar 10 ga watan Fabrairu a matsayin wa’adin amfani da tsofaffin takardun kudi na N200, N500 da N1,000.

A bisa karar da gwamnonin APC suka shigar, kotun koli ta bayar da umarnin dakatar da wa’adin, umarnin da gwamnatin tarayya ta yi watsi da shi.

Sai dai kuma wasu Jihohi biyu da PDP ke jagoranta su ma sun bi sahun gwamnatin tarayya.

Minista Keyamo, wanda kuma shi ne mai magana da yawun jam’iyyar APC na yakin neman zaben shugaban kasa, ya ce karar da gwamnatocin jihohin APC suka yi alama ce ta tarayya ta gaskiya.

Ya ce gwamnonin APC su tashi tsaye wajen adawa da gwamnatin tarayya kan wannan manufa, hakan ya nuna cewa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Bola Tinubu, idan aka zabe shi a ranar 25 ga watan Fabrairu a matsayin shugaban kasa, zai tabbatar da tsarin tarayya na gaskiya a kasar nan.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp