Home General Festus Keyamo ya yaba da jajircewar gwamnonin jam’iyyar APC kan sauyin takardun...

Festus Keyamo ya yaba da jajircewar gwamnonin jam’iyyar APC kan sauyin takardun kudi.

Karamin Ministan Kwadago da aiki Festus Keyamo ya yaba da jajircewar gwamnonin jam’iyyar APC da suka yi adawa da gwamnatin Muhammadu Buhari a kotun koli. Festus Keyamo, babban lauyan Najeriya, ya ce ta hanyar ayyukansu, gwamnonin APC suna “yaki ne da sunan talakawa, suna fafutukar ganin jama’a su samu taimako” a kan manufofin gwamnatin.

“Duk gwamnan da ya je kotu yana gwagwarmayar talakawa, yana fafutukar ganin jama’a su samu tallafi, dukkansu gwamnonin APC ne,”kalaman Minista  Keyamo.

A makon da ya gabata ne gwamnoni uku karkashin jam’iyyar APC, Kaduna, Kogi da Zamfara suka maka gwamnatin tarayya karkashin jam’iyyar APC a kotun koli, inda suka bukaci a sauya wa’adin da aka sanya na amfani da tsofaffin takardun kudi na naira. Babban bankin Najeriya ya sanya ranar 10 ga watan Fabrairu a matsayin wa’adin amfani da tsofaffin takardun kudi na N200, N500 da N1,000.

A bisa karar da gwamnonin APC suka shigar, kotun koli ta bayar da umarnin dakatar da wa’adin, umarnin da gwamnatin tarayya ta yi watsi da shi.

Sai dai kuma wasu Jihohi biyu da PDP ke jagoranta su ma sun bi sahun gwamnatin tarayya.

Minista Keyamo, wanda kuma shi ne mai magana da yawun jam’iyyar APC na yakin neman zaben shugaban kasa, ya ce karar da gwamnatocin jihohin APC suka yi alama ce ta tarayya ta gaskiya.

Ya ce gwamnonin APC su tashi tsaye wajen adawa da gwamnatin tarayya kan wannan manufa, hakan ya nuna cewa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Bola Tinubu, idan aka zabe shi a ranar 25 ga watan Fabrairu a matsayin shugaban kasa, zai tabbatar da tsarin tarayya na gaskiya a kasar nan.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp