Home General Festus Keyamo ya yaba da jajircewar gwamnonin jam’iyyar APC kan sauyin takardun...

Festus Keyamo ya yaba da jajircewar gwamnonin jam’iyyar APC kan sauyin takardun kudi.

Karamin Ministan Kwadago da aiki Festus Keyamo ya yaba da jajircewar gwamnonin jam’iyyar APC da suka yi adawa da gwamnatin Muhammadu Buhari a kotun koli. Festus Keyamo, babban lauyan Najeriya, ya ce ta hanyar ayyukansu, gwamnonin APC suna “yaki ne da sunan talakawa, suna fafutukar ganin jama’a su samu taimako” a kan manufofin gwamnatin.

“Duk gwamnan da ya je kotu yana gwagwarmayar talakawa, yana fafutukar ganin jama’a su samu tallafi, dukkansu gwamnonin APC ne,”kalaman Minista  Keyamo.

A makon da ya gabata ne gwamnoni uku karkashin jam’iyyar APC, Kaduna, Kogi da Zamfara suka maka gwamnatin tarayya karkashin jam’iyyar APC a kotun koli, inda suka bukaci a sauya wa’adin da aka sanya na amfani da tsofaffin takardun kudi na naira. Babban bankin Najeriya ya sanya ranar 10 ga watan Fabrairu a matsayin wa’adin amfani da tsofaffin takardun kudi na N200, N500 da N1,000.

A bisa karar da gwamnonin APC suka shigar, kotun koli ta bayar da umarnin dakatar da wa’adin, umarnin da gwamnatin tarayya ta yi watsi da shi.

Sai dai kuma wasu Jihohi biyu da PDP ke jagoranta su ma sun bi sahun gwamnatin tarayya.

Minista Keyamo, wanda kuma shi ne mai magana da yawun jam’iyyar APC na yakin neman zaben shugaban kasa, ya ce karar da gwamnatocin jihohin APC suka yi alama ce ta tarayya ta gaskiya.

Ya ce gwamnonin APC su tashi tsaye wajen adawa da gwamnatin tarayya kan wannan manufa, hakan ya nuna cewa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Bola Tinubu, idan aka zabe shi a ranar 25 ga watan Fabrairu a matsayin shugaban kasa, zai tabbatar da tsarin tarayya na gaskiya a kasar nan.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp