Home General Sojojin da ‘yan bindiga suka Hallaka a Jamhuriyyar Nijar yanzu haka sun...

Sojojin da ‘yan bindiga suka Hallaka a Jamhuriyyar Nijar yanzu haka sun Kai 17

Adadin sojojin da suka mutu a sakamakon harin kwanton bauna da ‘yan ta’adda su kai musu a jamhuriyar Nijar ya kai 17 kawo yanzu.

Tun farko dai ‘yan ta’addar sun hari sojojin ne a garin Tillaberi dake kudu maso yammacin kasar gab da kan iyakar kasar da Mali, inda nan take suka kashe sojoji 13, wasu 16 kuma suka yi batan dabo.

Ma’aikatar tsaron kasar ta cikin sanarwar da ta fitar, ta ce kawo yanzu an tabbatar da mutuwar sojoji 17, sai wasu 13 da suka jikkata, yayin da har yanzu ake ci gaba da neman guda 12.

Wannan yankin dama ya jima yana fama da ayyukan ‘yan ta’adda, yayin da ayyukan kungiyar Al-Qaeeda da na IS ya ta’azzara musamman daga shekarar 2017.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp