Home General Sojojin da ‘yan bindiga suka Hallaka a Jamhuriyyar Nijar yanzu haka sun...

Sojojin da ‘yan bindiga suka Hallaka a Jamhuriyyar Nijar yanzu haka sun Kai 17

Adadin sojojin da suka mutu a sakamakon harin kwanton bauna da ‘yan ta’adda su kai musu a jamhuriyar Nijar ya kai 17 kawo yanzu.

Tun farko dai ‘yan ta’addar sun hari sojojin ne a garin Tillaberi dake kudu maso yammacin kasar gab da kan iyakar kasar da Mali, inda nan take suka kashe sojoji 13, wasu 16 kuma suka yi batan dabo.

Ma’aikatar tsaron kasar ta cikin sanarwar da ta fitar, ta ce kawo yanzu an tabbatar da mutuwar sojoji 17, sai wasu 13 da suka jikkata, yayin da har yanzu ake ci gaba da neman guda 12.

Wannan yankin dama ya jima yana fama da ayyukan ‘yan ta’adda, yayin da ayyukan kungiyar Al-Qaeeda da na IS ya ta’azzara musamman daga shekarar 2017.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp