Home General NDLEA ta kama muggan ƙwayoyin da aka yi niyyar kai su Turai

NDLEA ta kama muggan ƙwayoyin da aka yi niyyar kai su Turai

Hukumar hana sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Najeriya, NDLEA ta ce ta ƙwace hodar ibilis da tabar wiwi, da wasu muggan ƙwayoyi da aka yi niyyar fitar da su zuwa Turai da wasu sassan na duniya.

A wani saƙo da hukumar ta wallafa a shafinta na Tuwita ta ce ta kama hodar ibilis da nauyinta ya kai kilogram 58, da kuma tabar wiwi a filayen jiragen saman Abuja da Legas da kuma wasu wurare a ƙasar.

Sanarwar ta ce jami’an hukumar sun kama wasu ‘yan kasuwa uku da take zargi da hannu a yankin Ojo da ke Legas

Haka kuma hukumar ta ce ta kwato ƙwayoyin Tramadol miliyan 2,684,900 da wasu magunguna a lokacin samamen da ta gabatar a makon da ya gabata a faɗin ƙasar.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp