Home General Masu sa ido kan zaɓe daga ƙasashen renon Ingila sun isa Najeriya

Masu sa ido kan zaɓe daga ƙasashen renon Ingila sun isa Najeriya

Masu sa ido a zaɓe daga ƙasashen renon Ingila sun iso Abuja, babban birnin Najeriya, gabanin babban zaɓen ƙasar na shugaban ƙasa da kuma ‘yan majalisar tarayya a ranar Asabar.

Kungiyar ta kunshi mutum 16 da suka fito daga ƙasashen renon Ingila wanda ya kunshi ‘yan siyasa da jami’an diflomasiyya da masana bangaren shari’a da masu kare hakkin ɗan adam da kuma daidaiton jinsi.

Da yake jawabi ga manema labarai a yau Litinin, shugaban kungiyar wada kuma shi ne tsohon shugaban Afirka ta Kudu, Thabo Mbeki, ya ce kudurinsu shi ne sa ido da kuma duba shirin da aka yi kafin zaɓe da ayyukan ranar zaɓe da kuma bayan zaɓe.

Mista Mbeki ya lura da cewa zaɓukan Najeriya za su kasance manya a nahiyar Afirka kuma sakamakonta na da matukar muhimmanci ga ɗaukacin nahiyar.

A don haka ya buƙaci jam’iyyun siyasa a ƙasar da ‘yan takara da kuma magoya bayansu da su tabbatar da ganin an yi zaɓukan ranar 25 ga watan Febrairu cikin koshin lafiya da kuma gaskiya.

An kiyasta cewa mutum miliyan 93.4 ne suka yi rajista domin samun damar kaɗa kuri’a a zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisar tarayya a cikin rumfunan zaɓe 176,846 da ke faɗin Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp