Home General An tabbatar da Mutuwar Sojojin Burkina Faso 50 sakamakon wani harin

An tabbatar da Mutuwar Sojojin Burkina Faso 50 sakamakon wani harin

Akalla sojojin Burkina Faso 51 ne aka tabbatar da cewa sun rasa rayukansu yayin da wasu da dama suka samu raunuka, sakamakon wani harin kwanton bauna da ‘yan ta’adda suka kai wa dakaru a yankin Sahel kamar dai yadda rundunar sojin kasar ta sanar a wannan litinin.

Wannan lamari dai ya faru ne a ranar juma’a da ta gabata, inda da farko aka ruwaito cewa sojoji 8 ne suka rasa rayukansu, kafin wata sanarwa da rundunar sojin kasar ta fitar a wannan litinin ta bayyana gano karin gawarwakin wasu 43 a inda lamarin ya faru.

Sanarwar ta ci gaba da cewa an kashe ‘yan ta’adda akalla 167, bayan da rundunar sojin saman kasar ta kai daukin gaggawa domin taimaka wa dakarunta.

Hakazalika sanarwar ta ce an lalata ko kuma kwace makamai da kuma babura masu tarin yawa wadanda ‘yan ta’addan ke amfani da su a gumurzun da aka yi tsakanin garuruwan Deou da Oursi da ke yakin na Sahel.

Burkina Faso dai ta jima tana fama da hare-haren masus ikirarin jihadi musamman a yankin Arewaci da kuma gabashin kasar, yayin da wannan barazana ke ci gaba da yaduwa hatta a wasu yankuna da ke kudancin kasar iyaka da Jamhuriyar Benin, Togo da kuma Ghana.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp