Home General ‘Yan takarar shugabancin Najeriya 18 sun sanya hannu a kan yarjejeniyar amincewa...

‘Yan takarar shugabancin Najeriya 18 sun sanya hannu a kan yarjejeniyar amincewa da sakamakon zaben 2023

‘Yan takarar shugabancin Najeriya 18 sun sanya hannu a kan yarjejeniyar amincewa da sakamakon zaben da za a yi ranar Asabar 25 ga watan nan na Fabarairu 2023.

Bisa tanadin yarjejeniyar, dukkanin ‘yan takarar sun amince cewa idan har ya kasance suna da wani ƙorafi kan zaɓen to za su bi hanyoyin da tsarin mulki ya tanada domin bi musu kadi.

Yarjejeniyar da aka yi a Abuja ranar Larabar nan wadda Kwamitin Zaman Lafiya na ƙasar ya shirye ta samu halartar dukkanin ‘yan takarar 18, tare da Shugaba Muhammadu Buhari, wanda za a gada.

Haka kuma tsohon shugaban ƙasar Kenya Uhuru Kenyata wanda shi ne jagoran masu sanya ido a zaɓen na Ƙungiyar Tarayyar Afirka, AU, da tsohon shugaban Afirka ta Kudu Thabo Mbeki duk sun halarta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Abin da Obi ya Fada Kan Atiku - Dele MomoduHukumar EFCC ta Gurfanar da Ma'aurata Kan Damfarar Kudi Kusan N2bnFiye da Kashi 60 na 'Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara - IMFGwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasartaƳan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a Katsina
X whatsapp