‘Yan takarar shugabancin Najeriya 18 sun sanya hannu a kan yarjejeniyar amincewa da sakamakon zaben da za a yi ranar Asabar 25 ga watan nan na Fabarairu 2023.
Bisa tanadin yarjejeniyar, dukkanin ‘yan takarar sun amince cewa idan har ya kasance suna da wani ƙorafi kan zaɓen to za su bi hanyoyin da tsarin mulki ya tanada domin bi musu kadi.
Read Also:
- Mawallafin PRNigeria Ya Fitar Da Littafin Tarihin Rayuwarsa Akan Rigimar NIPSS Yayin Da IMPR Ta Bayyana Cigaba Mai Karfi A Tsakiyar Shekara
- Shugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka Wajen Yaƙi da Ta’addanci
- Binciken Gaskiya: Shin Gajimaren ne ya ɓulɓulowa ƙasa a Hanyar Abuja Zuwa Kaduna?
Yarjejeniyar da aka yi a Abuja ranar Larabar nan wadda Kwamitin Zaman Lafiya na ƙasar ya shirye ta samu halartar dukkanin ‘yan takarar 18, tare da Shugaba Muhammadu Buhari, wanda za a gada.
Haka kuma tsohon shugaban ƙasar Kenya Uhuru Kenyata wanda shi ne jagoran masu sanya ido a zaɓen na Ƙungiyar Tarayyar Afirka, AU, da tsohon shugaban Afirka ta Kudu Thabo Mbeki duk sun halarta.










