Home General Za’a gudanar da zabe cikin lumana- Majalisar Tsaron Nijeriya

Za’a gudanar da zabe cikin lumana- Majalisar Tsaron Nijeriya

Majalisar tsaron Najeriya da shugaban Buhari ya jagoranta ta bayyana cewa za a gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisun dokoki na tarayya a ranar 25 ga watan Fabrairu, kamar yadda aka tsara.

Babban lauyan gwamnati kuma ministan shari’a na ƙasar Abubakar Malamin ne ya bayyana haka ga manema labarai jim kaɗan bayan kammala taron majalisar a fadar shugaban ƙasar.

Malami ya ce babban hafsan tsaro na ƙasar Janar Lucky Irabor, da hafsoshin rundunonin sojin ƙasar uku tare da babban sifeton ‘yan sandan ƙasar sun yi wa majalisar bayani game da shirin da suka yi kan babban zaɓen da ke tafe ranar Asabar mai zuwa.

Ya ƙara da cewa ”dangane da haka, majalisar ta haɗu a kan cewa zaɓen na ranar Asabar zai gudana kamar yadda aka tsara”.

Taron ya zo ne bayan, da taron majalisar magabata ta tabbatar da shirin hukumar zaɓen ƙasar da na ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro a kan zaɓen na ranar Asabar mai zuwa.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Abin da Obi ya Fada Kan Atiku - Dele MomoduHukumar EFCC ta Gurfanar da Ma'aurata Kan Damfarar Kudi Kusan N2bnFiye da Kashi 60 na 'Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara - IMFGwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasartaƳan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a Katsina
X whatsapp