Home General Za’a gudanar da zabe cikin lumana- Majalisar Tsaron Nijeriya

Za’a gudanar da zabe cikin lumana- Majalisar Tsaron Nijeriya

Majalisar tsaron Najeriya da shugaban Buhari ya jagoranta ta bayyana cewa za a gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisun dokoki na tarayya a ranar 25 ga watan Fabrairu, kamar yadda aka tsara.

Babban lauyan gwamnati kuma ministan shari’a na ƙasar Abubakar Malamin ne ya bayyana haka ga manema labarai jim kaɗan bayan kammala taron majalisar a fadar shugaban ƙasar.

Malami ya ce babban hafsan tsaro na ƙasar Janar Lucky Irabor, da hafsoshin rundunonin sojin ƙasar uku tare da babban sifeton ‘yan sandan ƙasar sun yi wa majalisar bayani game da shirin da suka yi kan babban zaɓen da ke tafe ranar Asabar mai zuwa.

Ya ƙara da cewa ”dangane da haka, majalisar ta haɗu a kan cewa zaɓen na ranar Asabar zai gudana kamar yadda aka tsara”.

Taron ya zo ne bayan, da taron majalisar magabata ta tabbatar da shirin hukumar zaɓen ƙasar da na ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro a kan zaɓen na ranar Asabar mai zuwa.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mawallafin PRNigeria Ya Fitar Da Littafin Tarihin Rayuwarsa Akan Rigimar NIPSS Yayin Da IMPR Ta Bayyana Cigaba Mai Karfi A Tsakiyar ShekaraShugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka Wajen Yaƙi da Ta'addanciBinciken Gaskiya: Shin Gajimaren ne ya ɓulɓulowa ƙasa a Hanyar Abuja Zuwa Kaduna?HRW ta Zargin Hukumomin Najeriya da Rashin Adalci ga Ƴan  ƙungiyar Boko HaramHukuncin da Kotu ta Yanke wa Matashin da ya  Yunƙurin Satar Motar Yan SandaMutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto 
X whatsapp