Home General Za’a gudanar da zabe cikin lumana- Majalisar Tsaron Nijeriya

Za’a gudanar da zabe cikin lumana- Majalisar Tsaron Nijeriya

Majalisar tsaron Najeriya da shugaban Buhari ya jagoranta ta bayyana cewa za a gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisun dokoki na tarayya a ranar 25 ga watan Fabrairu, kamar yadda aka tsara.

Babban lauyan gwamnati kuma ministan shari’a na ƙasar Abubakar Malamin ne ya bayyana haka ga manema labarai jim kaɗan bayan kammala taron majalisar a fadar shugaban ƙasar.

Malami ya ce babban hafsan tsaro na ƙasar Janar Lucky Irabor, da hafsoshin rundunonin sojin ƙasar uku tare da babban sifeton ‘yan sandan ƙasar sun yi wa majalisar bayani game da shirin da suka yi kan babban zaɓen da ke tafe ranar Asabar mai zuwa.

Ya ƙara da cewa ”dangane da haka, majalisar ta haɗu a kan cewa zaɓen na ranar Asabar zai gudana kamar yadda aka tsara”.

Taron ya zo ne bayan, da taron majalisar magabata ta tabbatar da shirin hukumar zaɓen ƙasar da na ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro a kan zaɓen na ranar Asabar mai zuwa.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp