Home General kotun majistare a jihar Kano ta aike da Alhassan Ado Duguwa...

kotun majistare a jihar Kano ta aike da Alhassan Ado Duguwa zuwa gidan gyaran hali

Wata kotun majistare a jihar Kano ta aike da shugaban masu rinjaye na majalisar wakilan Najeriya Alhassan Ado Duguwa zuwa gidan yari bayan gurfanar da shi a gaban kotun.
Ana zargin ɗan majalisar da muggan laifuka ciki har da zargin aikata kisan kai da mallakar makami ba bisa ƙa’ida ba da hannu a kunna wuta a wani gini wadda tayi sanadiyyar mutuwar wasu mutane tare da raunata wasu.
An gurfanar da shi gaban kotu mai lamba 54 dake No man’s land  tare da wani mutum wanda ake zargi sun haɗa baki wajen aikata kisan kai da tayar da zaune-tsaye a ƙaramar hukumar Tudun wada da ke jihar ranar Asabar da ta gabata.
Alƙalin kotun ya ɗage shari’ar zuwa ranar 7 ga watan Maris domin duba buƙatar yiyuwar bayar da belin ɗan majalisar ko kuma akasin haka.
Bayan fitowa daga kotun ne tashar PRNigeria ta sami zarafin tattaunawa da lauyan gwamnatin jihar kano Bar Lamido Abba Soron Dinki inda ya bayyana cewa yanzu haka za su yi Nazari kafin ranar da koton ta sanya a dawo domin cigaba da sauraren karar.
Shima a nasa bangaren lauyan dake kare wanda ake tuhuma Bar. Abdul Adamu Fagge ya bayyana dalilan da ya sanyasu bukatar kotun ta bayar da belin na Alhasan Ado Doguwa.
Akwai lauyoyin masu tarin yawa dake sanya idanu kan Shari’ar a karkashin Barista Mutari Dandago.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp