Home General Rundunar ‘Yan sandan Jihar kano ta zargi wasu da amfani da ‘yan...

Rundunar ‘Yan sandan Jihar kano ta zargi wasu da amfani da ‘yan Daba a zaben Gwamna dake tafe

Rundunar ‘yan sanda a jihar Kano ta ce ta samu bayanai da ke nuna cewa wasu ‘yan siyasa na shirin shigo da ‘yan bangar siyasa zuwa jihar domin tayar da hatsaniya a zaɓen gwamnoni da na ‘yan majalisar dokoki da ke tafe.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Mamman Dauda shi ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar, inda ya ce ‘yan siyasa da ke ganin za su fadi, tuni suka shirya tayar da tarzoma a zaɓen da ke tafe a ranar Asabar.

Sai dai, Mamman Dauda, ya gargaɗi dukkan ‘yan bangar siyasa da wasu ɓata gari cewa kada su kuskura su ta da fitina saboda a shirye ‘yan sanda suke wajen hukunta duk wanda aka kama da laifi.

CP Dauda ya kuma ce rundunar tare da haɗin gwiwar wasu jami’an tsaro a jihar za su tabbatar da cewa an kama dukkan waɗanda ake zargi, inda ya ce duk ɗan bangar siyasa da aka kama, za a tura shi zuwa kotu tare da waɗanda suka saka su aikin.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp