Home General Rundunar ‘Yan sandan Jihar kano ta zargi wasu da amfani da ‘yan...

Rundunar ‘Yan sandan Jihar kano ta zargi wasu da amfani da ‘yan Daba a zaben Gwamna dake tafe

Rundunar ‘yan sanda a jihar Kano ta ce ta samu bayanai da ke nuna cewa wasu ‘yan siyasa na shirin shigo da ‘yan bangar siyasa zuwa jihar domin tayar da hatsaniya a zaɓen gwamnoni da na ‘yan majalisar dokoki da ke tafe.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Mamman Dauda shi ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar, inda ya ce ‘yan siyasa da ke ganin za su fadi, tuni suka shirya tayar da tarzoma a zaɓen da ke tafe a ranar Asabar.

Sai dai, Mamman Dauda, ya gargaɗi dukkan ‘yan bangar siyasa da wasu ɓata gari cewa kada su kuskura su ta da fitina saboda a shirye ‘yan sanda suke wajen hukunta duk wanda aka kama da laifi.

CP Dauda ya kuma ce rundunar tare da haɗin gwiwar wasu jami’an tsaro a jihar za su tabbatar da cewa an kama dukkan waɗanda ake zargi, inda ya ce duk ɗan bangar siyasa da aka kama, za a tura shi zuwa kotu tare da waɗanda suka saka su aikin.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp