Home General INEC ta cire sunan Doguwa daga jerin zaɓaɓɓun ‘yan majalisun tarayya

INEC ta cire sunan Doguwa daga jerin zaɓaɓɓun ‘yan majalisun tarayya

Hukumar zaɓen Najeriya ta cire sunan shugaban masu rinjaye na majalisar wakilan Najeriya Alhassan Ado Doguwa daga cikin jerin sunayen zaɓaɓɓeun ‘yan majalisar wakilan ƙasar da suka yi nasara a zaɓen da aka gudanar cikin watan Fabrairu.

Hukumar zaɓen ƙasar ce dai tun da farko ta ayyana shi a matsayin wanda ya yi nasara a zaɓen ɗan majalisar wakilai ta tarayya mai wakiltar mazaɓar Doguwa da Tudunwada a jihar Kano da ke arewacin Najeriya.

Jami’in tattara sakamakon zaɓen Farfesa Ibrahim Adamu Yakasai ya bayyana cewa Doguwa na jam’iyyar APC ya samu ƙuri’a 39,732, inda abokin takararsa na jam’iyyar NNPP Yushau Salisu Abdullahi ya samu ƙuri’a 34,798.

To sai dai a jerin sunayen zaɓaɓɓun ‘yan majalisun da hukumar zaɓen ta fitar a shafinta na Twitter, babu sunan Alhassan Ado Doguwa a cikin jerin ‘yan majalisun.

INEC ɗin ta ce an tilasta wa jami’in tattara sakamakon zaɓen wajen bayyana sakamakon da ya bai wa Doguwa nasara a zaɓen da aka gudanar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp