Home Labarai ‘Yan bindiga sun hallaka jami’an tsaron sa kai 6 a jihar Kaduna

‘Yan bindiga sun hallaka jami’an tsaron sa kai 6 a jihar Kaduna

Rahotannin daga jihar Kaduna na bayyana cewa wasu ‘yan bindiga sun hallaka jami’an tsaron sa kai na bijilanti 6 a shingen binciken ababawan hawa na Awaro dake yammacin birnin-Gwari, a karamar hukumar birnin Gwari ta jihar Kaduna dake arewa maso yammacin Nijeria.
Jaridar Punch ta ruwaito cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 4 na yammacin ranar laraba.
Guda cikin Jami’an bijilantin Usman Babangida, ya tabbatarwa da maneman labarai mutuwar abokan aikin nasa a ranar laraba sakamakon harin ‘yan bindiga a shingen binciken Ababan hawa da suke gudanar da ayyukan su.
Inda yace ‘yan bindigar sun fara harfi kan mai uwa da wabi bayan sun hangi jami’an na bijilanti, in da suka hallaka 6 daga cikin su, ya kuma ce wadanda aka hallaka din anyi jana’idar su kamar yadda addinin musulunci yayi tanadi.
Yace lamarin ya faru ne jim kadan bayan da ‘yan bindiag suka yi wani artabu da wasu ‘yan bindiga a wani kauye dake kusa da sum ai suna Bugai.
Ko da PRNigeria ta tuntubi kakakin rundunar ‘yan sanda jihar Kaduna Muhammad Jalige ta wayar tarho bata same shi ba.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp