Home Labarai ‘Yan bindiga sun hallaka jami’an tsaron sa kai 6 a jihar Kaduna

‘Yan bindiga sun hallaka jami’an tsaron sa kai 6 a jihar Kaduna

Rahotannin daga jihar Kaduna na bayyana cewa wasu ‘yan bindiga sun hallaka jami’an tsaron sa kai na bijilanti 6 a shingen binciken ababawan hawa na Awaro dake yammacin birnin-Gwari, a karamar hukumar birnin Gwari ta jihar Kaduna dake arewa maso yammacin Nijeria.
Jaridar Punch ta ruwaito cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 4 na yammacin ranar laraba.
Guda cikin Jami’an bijilantin Usman Babangida, ya tabbatarwa da maneman labarai mutuwar abokan aikin nasa a ranar laraba sakamakon harin ‘yan bindiga a shingen binciken Ababan hawa da suke gudanar da ayyukan su.
Inda yace ‘yan bindigar sun fara harfi kan mai uwa da wabi bayan sun hangi jami’an na bijilanti, in da suka hallaka 6 daga cikin su, ya kuma ce wadanda aka hallaka din anyi jana’idar su kamar yadda addinin musulunci yayi tanadi.
Yace lamarin ya faru ne jim kadan bayan da ‘yan bindiag suka yi wani artabu da wasu ‘yan bindiga a wani kauye dake kusa da sum ai suna Bugai.
Ko da PRNigeria ta tuntubi kakakin rundunar ‘yan sanda jihar Kaduna Muhammad Jalige ta wayar tarho bata same shi ba.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp