Home Labarai ‘Yan bindiga sun hallaka jami’an tsaron sa kai 6 a jihar Kaduna

‘Yan bindiga sun hallaka jami’an tsaron sa kai 6 a jihar Kaduna

Rahotannin daga jihar Kaduna na bayyana cewa wasu ‘yan bindiga sun hallaka jami’an tsaron sa kai na bijilanti 6 a shingen binciken ababawan hawa na Awaro dake yammacin birnin-Gwari, a karamar hukumar birnin Gwari ta jihar Kaduna dake arewa maso yammacin Nijeria.
Jaridar Punch ta ruwaito cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 4 na yammacin ranar laraba.
Guda cikin Jami’an bijilantin Usman Babangida, ya tabbatarwa da maneman labarai mutuwar abokan aikin nasa a ranar laraba sakamakon harin ‘yan bindiga a shingen binciken Ababan hawa da suke gudanar da ayyukan su.
Inda yace ‘yan bindigar sun fara harfi kan mai uwa da wabi bayan sun hangi jami’an na bijilanti, in da suka hallaka 6 daga cikin su, ya kuma ce wadanda aka hallaka din anyi jana’idar su kamar yadda addinin musulunci yayi tanadi.
Yace lamarin ya faru ne jim kadan bayan da ‘yan bindiag suka yi wani artabu da wasu ‘yan bindiga a wani kauye dake kusa da sum ai suna Bugai.
Ko da PRNigeria ta tuntubi kakakin rundunar ‘yan sanda jihar Kaduna Muhammad Jalige ta wayar tarho bata same shi ba.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp