Home Labarai Buhari ya koma Abuja daga Daura

Buhari ya koma Abuja daga Daura

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya koma fadar gwamnatinsa da ke Abuja, bayan shafe kwanaki a mahaifarsa Daura ta jihar Katsina a arewa maso yammacin Najeriya.

Wannan na cikin wani sako da mai magana da yawun shugaban Malam Garba Shehu ya wallafa a shafinsa ta Twitter, inda ya ce shugaban ya koma Abuja ne bayan kwanaki 18.

Saƙon ya ƙara da cewa shugaban ya yi amfani da lokacin wajen gudanar da zaɓen shugaban ƙasa tare da ziyara da ya kai Maiduguri da taron Majalisar Dinkin Duniya da ya halarta a birnin Doha na ƙasar Qatar.

Garba Shehu ya ƙara da cewa nan gaba kaɗan ne cikin wannan makon shugaban tare da sauran ma’aikatan fadarsa da suka yi rajistar zaɓe a Daura za su sake komawa domin halartar zaɓen gwamnoni da na ‘yan majalisun dokokin jihohi.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp