Home Labarai Buhari ya koma Abuja daga Daura

Buhari ya koma Abuja daga Daura

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya koma fadar gwamnatinsa da ke Abuja, bayan shafe kwanaki a mahaifarsa Daura ta jihar Katsina a arewa maso yammacin Najeriya.

Wannan na cikin wani sako da mai magana da yawun shugaban Malam Garba Shehu ya wallafa a shafinsa ta Twitter, inda ya ce shugaban ya koma Abuja ne bayan kwanaki 18.

Saƙon ya ƙara da cewa shugaban ya yi amfani da lokacin wajen gudanar da zaɓen shugaban ƙasa tare da ziyara da ya kai Maiduguri da taron Majalisar Dinkin Duniya da ya halarta a birnin Doha na ƙasar Qatar.

Garba Shehu ya ƙara da cewa nan gaba kaɗan ne cikin wannan makon shugaban tare da sauran ma’aikatan fadarsa da suka yi rajistar zaɓe a Daura za su sake komawa domin halartar zaɓen gwamnoni da na ‘yan majalisun dokokin jihohi.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp