Home Labarai NAPTIP ta kuɓutar da mata 11 da aka yi niyyar safararsu zuwa...

NAPTIP ta kuɓutar da mata 11 da aka yi niyyar safararsu zuwa Libya

Hukumar yaƙi da fataucin bil-Adama a Najeriya NAPTIP ta ce tana gudanar da bincike kan lamarin da ya kai ga safarar wasu mata ‘yan Najeriya 11 daga ƙasar.

An ceto ‘yan matan ne a makwaɓciyar ƙasar Jamhuriyar Nijar lokacin da wata ƙungiyar masu safarar mutane ke niyyar jigilar su zuwa ƙasar Libya.

Ƴan matan da suka kasance dukkaninsu matasa, an dawo da su gida Najeriya tare da miƙa su ga hukumar hana fataucin mutane ta kasa NAPTIP reshen Sokoto.

Kwamandan NAPTIP na shiyyar Sokoto, Abubakar Tabra ya shaida wa BBC cewa jami’an hukumar kula da shige da fice ta ƙasa reshen Illela ne suka karɓi ‘yan matan a karshen makon da ya gabata, inda ya ce a yanzu sun soma bincike da nufin kamo waɗanda ake zargi da safarar ƴan matan.

Ya kuma ce ana kuma kokarin bincike don gano ‘yan uwan ƴan matan don sake haɗa su da iyalansu.

Bayanan da aka tattara sun nuna cewa waɗanda abin ya rutsa da su sun fito ne daga kudancin Najeriya.

Rahotanni sun ce an sace musu wayoyinsu da kayayyakinsu a cikin dazukan Jamhuriyar Nijar, inda waɗanda suka yi safararsu suka yi watsi da su, kafin jami’an ‘yan sandan Nijar ɗin su kuɓutar da su tare da miƙa su ga jami’an shige da fice na Najeriya da ke kan iyaka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp