Home Labarai Rundunar ‘Yan Sanda ta Jihar kano ta haramta bikin murnar lashe zabe

Rundunar ‘Yan Sanda ta Jihar kano ta haramta bikin murnar lashe zabe

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano ƙarƙashin jagorancin CP Usaini Mohammed Gumel mai jagorantar harkokin zaɓen da ke gudana a jihar, ta haramta bikin murnar lashe ta hanyar zagaye kan tituna ko makamancin haka wanda ka iya haifar da hargitsi a jihar.

Kwamishinan ya bayyana haka ga manema labarai a yammacin Asabar bayan kammala zagayen da haɗakar rundunonin tsaro da suka gabatar na sa ido bisa yadda dokar Hukumar ‘Yan Sanda ta Ƙasa, ƙarƙashin jagorancin IG Usman Baba Alkali ta ɗora ma kowane kwamishina a faɗin ƙasar a lokacin zaɓen.

CP Gumel ya kuma yaba da yadda jama’a a jihar Kano suka karɓi shawarwari na a yi zaɓe cikin kwanciyar hankali, inda ya ce farkon zagaye da rundunar ta fara da sauran shugabanin jami’an tsaro sun isa wuraren da ake gudanar da zaɓe inda masu zaɓe suka yi farin cikinsu.

“Mun kuma ga ƙananan yara da ba su isa zaɓe ba a cikin guraren zaɓe inda muka ga bai kamata a ce ana barin su ba dan ana iya samu ‘yan sane da yankan aljihu ko kuma wani ɓata-gari ya yi amfani da su wajen tada husuma a lokacin gudanar da zaɓen.

“Ina roƙon jama’ar jihar Kano yadda aka bada haɗin kai wajen kaɗa ƙuri’a, nan ma ina kira da roƙo kan a ƙara bada goyon baya har lokacin da hukumar zaɓe za ta bayyana wanda ya ci zaɓe ya kasance an taya shi murna ta fuskar da ta dace.

Daga ƙarshe, ya yi jan hankali kan duk wanda ya fito murnar lashe zaɓe da manufar cin zarafin wani, ya sani hukuma ba za ta ƙyame shi ba.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp