Home Labarai Masu amfani da intanet a Kano sun haura miliyan 8

Masu amfani da intanet a Kano sun haura miliyan 8

Hukumar ƙididdiga ta ƙasa ta ce layukan wayar salula miliyan 222.6 ake da su a ɗaukacin Najeriya a ƙarshen shekara ta 2022.

Alƙaluma sun nuna cewa an samu ƙarin layukan wayoyin salula miliyan 27.1 a kan miliyan 195.5 da ake da su a ƙarshen 2021.

Hukumar ƙididdiga ce ta fitar da alƙaluman a cikin bayananta kan masu amfani da wayoyin tarho a cikin wani rahoto na watanni ukun ƙarshe shekara ta 2022.

Rahoton ya kuma ce jimillar masu amfani da intanet sosai ya kai miliyan 154.9 a ƙarshen 2022, idan an kwatanta da miliyan 142 da ake da su a ƙarshen 2021.

Game da ƙididdigar masu amfani da wayoyin salula a tsakanin jihohi, rahoton ya nuna cewa Lagos ce jiha mafi yawan layukan wayar salula da 26.5 a ƙarshen 2022, sai jihar Ogun da ke biye mata da miliyan 13.

Kano ce jihar da ta zo a mataki na uku da layukan wayar salula miliyan 12.4.

Rahoton ya nuna cewa jihar Bayelsa mafi ƙarancin layukan wayar salula da miliyan 1.6 sai jihar Ebonyi mai layukan waya miliyan 1.9, akwai kuma jihar Ekiti mai layuka miliyan biyu.

Haka zalika, ya nuna jihar Lagos ce mafi yawan masu amfani da intanet da miliyan 18.7 sai jihar Ogun mai miliyan 9.2 sai kuma jihar Kano mai miliyan 8.5.

Bayelsa ce jiha mafi ƙarancin masu amfani da intanet da miliyan 1.1, tana ƙasan Ebonyi mai miliyan 1.3 ga kuma Ekiti mai miliyan ɗaya da rabi.

Rahoton ya nuna cewa mafi yawan masu layukan wayar salula a Najeriya da MTN suke aiki a shekara ta 2022.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp