Home Labarai Sojojin Nijeriya sun sake kubutar ‘yan matan Chibok

Sojojin Nijeriya sun sake kubutar ‘yan matan Chibok

Dakarun Sojojin Nijeriya sun sami nasarar sake kubutar da karin ‘yan Matan Chibok tare da hallaka ‘yan Ta’ adda 40 – DHQ

Shalkwatar rundunar sojin Nijeriya tace dakarun hadin Guiwa na Operation HADARIN DAJI, dake aikin samar da tsaron a yankin Arewa maso gabashin Nijeriya, sun sami nasarar kama ‘yan Ta’adda 5 tre da kubutar da fararen hula 121 da suka hadar da yara 72 da mata 49 cikin su akwai ‘yan matan makarantar Chibok 2.

Babban hafsan sojojin kasar Laftanal Janar Lucky Irabor ne ya bayyana  hakan yayin da yake bayyana irin nasarorin da rundunar ta samu kamar yadda aka saba mako mako.

Daraktar yada labaran rundunar Manjo Janar Musa Danmadani yayi jawabi dalla-dalla bisa ayyukan dakarun, inda yace dakarun sojin sama dana kasa dake cikin rundunar Operation HADARIN DAJI dake gudanar da ayyukan su a yankin Arewa maso yammacin kasar sun kama wadanda ake zargin ‘yan bindiga ne masu safar kwayoyi a kauyen Wazata dake karamar hukumar birnin Gwari ta jihar Kaduna.

Haka kuma a Arewa maso gabashi dakarun sun sami nasarar hallaka mayaka Boko Haram dana ISWAP 40, tare da kama 25 wanda suka hadar da masu yi musu safarar kayayyaki da baya ai a lokacin da suka shirya kai hare hare kan kauyuka da dazukan garuruwan Gwoza, Bama, Biu, Kukawa, Monguno, Marte, Damboa, Mobbar da yankunan karamar hukumar Konduga a jihar Borno State.

PRNigeria hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp