Home Labarai Sojojin Nijeriya sun sake kubutar ‘yan matan Chibok

Sojojin Nijeriya sun sake kubutar ‘yan matan Chibok

Dakarun Sojojin Nijeriya sun sami nasarar sake kubutar da karin ‘yan Matan Chibok tare da hallaka ‘yan Ta’ adda 40 – DHQ

Shalkwatar rundunar sojin Nijeriya tace dakarun hadin Guiwa na Operation HADARIN DAJI, dake aikin samar da tsaron a yankin Arewa maso gabashin Nijeriya, sun sami nasarar kama ‘yan Ta’adda 5 tre da kubutar da fararen hula 121 da suka hadar da yara 72 da mata 49 cikin su akwai ‘yan matan makarantar Chibok 2.

Babban hafsan sojojin kasar Laftanal Janar Lucky Irabor ne ya bayyana  hakan yayin da yake bayyana irin nasarorin da rundunar ta samu kamar yadda aka saba mako mako.

Daraktar yada labaran rundunar Manjo Janar Musa Danmadani yayi jawabi dalla-dalla bisa ayyukan dakarun, inda yace dakarun sojin sama dana kasa dake cikin rundunar Operation HADARIN DAJI dake gudanar da ayyukan su a yankin Arewa maso yammacin kasar sun kama wadanda ake zargin ‘yan bindiga ne masu safar kwayoyi a kauyen Wazata dake karamar hukumar birnin Gwari ta jihar Kaduna.

Haka kuma a Arewa maso gabashi dakarun sun sami nasarar hallaka mayaka Boko Haram dana ISWAP 40, tare da kama 25 wanda suka hadar da masu yi musu safarar kayayyaki da baya ai a lokacin da suka shirya kai hare hare kan kauyuka da dazukan garuruwan Gwoza, Bama, Biu, Kukawa, Monguno, Marte, Damboa, Mobbar da yankunan karamar hukumar Konduga a jihar Borno State.

PRNigeria hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp