Home Labarai NiMet ta yi gargaɗi kan samun ruwan sama mai karfi a arewacin...

NiMet ta yi gargaɗi kan samun ruwan sama mai karfi a arewacin Najeriya

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargadin samun ruwan sama mai karfin gaske gami da tsawa a wasu sassa na arewa maso gabashin Najeriya.

Kakakin hukumar, Muntari Ibrahim ne ya bayyana haka ta cikin wata sanarwa da ya fitar.

A cewarsa, jihohin da za su fuskanci wannan yanayi sun hada da Borno da Adamawa da Gombe da kuma Taraba.

Sannan sanarwar ta kuma ce za a samu ruwa tafe da iska a jihohi irinsu Gombe da Bauchi da Benue da Filato da Nasarawa da Enugu da Ebonyi.

Sai wasu kuma jihohin kudanci. Rahoton ya ce za a shafe tsawon sa’a uku zuwa shida ana tafka ruwan.

Nimet ta shawarci mutane suyi takatsan-tsan da kasancewa masu kula saboda tsaronsu.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp