Home Labarai Gwamnan jihar kano ya cire kuɗin makarantar Gidan kangararro ta Kiru

Gwamnan jihar kano ya cire kuɗin makarantar Gidan kangararro ta Kiru

Gwamnan jihar kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya yi alkawarin gyarawa da inganta cibiyar gyaran hali da tarbiyya deke karamar hukumar Kiru domin magance matsalolin shaye-shaye da matasa ke yi a jihar kano.

Gwamnan ya bayyana hakan ne lokacin da ya ziyarci cibiyar domin ganin matsalolin da take fuskanta da kuma duba yadda za’a magance su.

Gwamnan yace gwamnatin sa zata Maida hankali wajen inganta rayuwar matasa domin su ne kashin bayan cigaban al’umma.

Yace shaye-shayen miyagun kwayoyi shi ke haddasa matsaloli na ta’addanci rashin tsaro da saura laifuffuka a cikin al’umma, a don haka yace zai inganta cibiyar ta hanyar samar da ababen more rayuwa da Kuma abincin da matasan dake gidan zasu rika ci.

Wannan ziyarana matsayin aikin Gwamnan na farko bayan rantsar da shi , yace gwamnati ta daukewa Iyayen da yaransu suke karɓar horo, tare da umartar Babbar Sakatariyar ta ma’aikatar mata da ta rubuto masa matsalolin da cibiyar take fuskanta domin magance wa nan da wata guda.

Da take nata jawabin Babbar Sakatariyar ma’aikatar mata ta jihar kano Dr. Sa’adatu Sa’idu Bala ta godewa sabon gwamnan saboda ziyarar da yakai cibiyar wanda tace hakan ya nuna yadda ya damu da halin da matasa ke ciki a jihar kano musamman batun kwacen waya da ake kashe mutane akai.

Babbar Sakatariyar ta bayyana cewa cibiyar tana taka rawa wajen gyara rayuwar matasa ta hanyar basu magani da koya musu sana’o’in dogaro da don inganta rayuwar su. Ta kuma ce cibiyar tana fuskantar matsaloli masu tarin yawa.

Tace ana gudanar da makarantar ne daga Naira 70 da ake biyawa yaran duk wata da kuma Naira dubu dari 5 da tsohuwar gwamnatin kano take ba su.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp