Home Labarai Gwamnatin Borno za ta ɗauki malamai 5,000 aiki da dawo da karatun...

Gwamnatin Borno za ta ɗauki malamai 5,000 aiki da dawo da karatun yamma

Gwamnar jihar Borno, Babagana Zulum ya ce za a dauki malamai 5,000 aiki don fara karatun firamare da sakandare da rana domin magance matsololin cunkoso da kuma rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta.

Zulum ya bayyana hakan ne a ranar Litinin a Maiduguri yayin jawabinsa na farko bayan rantsar da shi karo na biyu.

Ya ce : “Duk da cewa mun gina sabbin makarantu masu girman gaske tare da fadada makarantun da ake da su da sabbin ajujuwa kusan 1,000, amma har yanzu muna fuskantar matsalar cunkoso a ajujuwa, kuma muna fama da matsalar da dubban yara da ba sa zuwa makaranta”

“Ina mai farin cikin sanar da cewa nan ba da jimawa ba jihar Borno za ta fara tsarin makarantun firamare da sakandare na rana. Na nada kwamitin aiwatarwa da zai tsara hanyoyin da za a fara karatun makarantun la’asar, kuma zai tantance makarantun gwajin da za a zabo daga wasu manyan makarantunmu na Maiduguri da ke da lantarki.”

Zulum ya bayyana cewa bullo da tsarin karatun na yamma zai bukaci karin ma’aikata, don haka ya umurci ofishin shugaban ma’aikata da ya zakulo wasu kwararrun ma’aikatan da a halin yanzu ba sa aiki a sakatariyar gwamnati, wadanda za a horar da su kan sanin makamar aikin.

Gwamnan ya kuma ce za a dauki matakan tsaro domin tabbatar da samun nasarar makarantun na yamma, yana mai cewa a wasu lokutan ana iya daukar darasi har zuwa farkon dare.

Zulum ya ce za a sake bullo da wasu matakai kamar jarrabawar gwaji da ake kira ”Mock” da Ingilishi a makarantun sakandare tare da kafa cibiyoyi daukar jarrabawa masu inganci ta yadda gwamnati za ta iya gano baiwa da fasihar yaran.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp