Home Labarai Tinubu ya sanya hannu kan dokar bai wa ɗalibai bashi

Tinubu ya sanya hannu kan dokar bai wa ɗalibai bashi

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya sanya hannu kan dokar bai wa ɗalibai bashin karatu ta ƙasa.

Mai magana da yawun Gwamnatin Tarayya, Dele Alake ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya fitar yau Litinin.

Sanarwar ta ce za a ajiye kuɗaɗen da za a rinƙa bayar da bashin ne a asusun Ma’aikatar Ilimi, kuma ɗaliban manyan makarantu ne kawai za su iya cin gajiyarsu.

Mako biyu da suka gabata ne ƙudirin, wanda shugaban Majalisar Wakilan Tarayya, Femi Gbajabiamila ya gabatar, ya tsallake karatu na uku a Majalisar Dokokin Tarayya.

Dokar za ta bai wa ɗalibai ƴan asalin Najeriya damar karɓar bashi cikin sauƙi, wanda babu ruwa a tattare da shi daga Asusun Bayar da Bashin Karatu na Najeriya.

PRNigeria hausa I

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp