Home Labarai Najeriya ta sake komawa ta ɗaya wajen fitar da ɗanyen mai a...

Najeriya ta sake komawa ta ɗaya wajen fitar da ɗanyen mai a Afirka

Najeriya ta sake komawa matsayinta ta ɗaya a cikin jerin ƙasashe masu fitar da ɗanyen mai bayan da ta samu ƙari a yawan ɗanyen man da take fitarwa a kowace rana.

A watan Mayu, alƙaluma sun sun nuna cewa Najeriya ta rinƙa fitar da ɗanyen mai ganga miliyan 1.184.

Alƙaluman wata-wata da Ƙungiyar Ƙasashe Masu Fitar da Man Fetur da Duniya (OPEC) ta fitar sun nuna cewa Najeriya ta ɗara Libya, mai fitar da ganga miliyan 1,158, da Angola mai fitar da ganga miliyan 1,111, da kuma Algeria mai fitar da ganga 962,000.

A cikin shekarar nan ta 2023 ne dai yawan ɗanyen man da Najeriya ke fitarwa zuwa ƙasashen ƙetare ya ragu matuƙa, inda ya koma ganga 999,000 a kowace rana, lamarin da ya mayar da ita bayan ƙasashen Libya da Angola da Algeria.

Najeriya dai na fama da matsalar masu satar ɗanyen mai, da rashin tsaro a yankin Neja-Delta mai arziƙin man fetur, da fasa bututan mai, waɗanda gwamnati ta ce su ne manyan dalilan da suka sanya fitar da ɗanyen man ya yi ƙasa sosai.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp