Home Labarai Najeriya ta sake komawa ta ɗaya wajen fitar da ɗanyen mai a...

Najeriya ta sake komawa ta ɗaya wajen fitar da ɗanyen mai a Afirka

Najeriya ta sake komawa matsayinta ta ɗaya a cikin jerin ƙasashe masu fitar da ɗanyen mai bayan da ta samu ƙari a yawan ɗanyen man da take fitarwa a kowace rana.

A watan Mayu, alƙaluma sun sun nuna cewa Najeriya ta rinƙa fitar da ɗanyen mai ganga miliyan 1.184.

Alƙaluman wata-wata da Ƙungiyar Ƙasashe Masu Fitar da Man Fetur da Duniya (OPEC) ta fitar sun nuna cewa Najeriya ta ɗara Libya, mai fitar da ganga miliyan 1,158, da Angola mai fitar da ganga miliyan 1,111, da kuma Algeria mai fitar da ganga 962,000.

A cikin shekarar nan ta 2023 ne dai yawan ɗanyen man da Najeriya ke fitarwa zuwa ƙasashen ƙetare ya ragu matuƙa, inda ya koma ganga 999,000 a kowace rana, lamarin da ya mayar da ita bayan ƙasashen Libya da Angola da Algeria.

Najeriya dai na fama da matsalar masu satar ɗanyen mai, da rashin tsaro a yankin Neja-Delta mai arziƙin man fetur, da fasa bututan mai, waɗanda gwamnati ta ce su ne manyan dalilan da suka sanya fitar da ɗanyen man ya yi ƙasa sosai.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp