Home Labarai Najeriya ta sake komawa ta ɗaya wajen fitar da ɗanyen mai a...

Najeriya ta sake komawa ta ɗaya wajen fitar da ɗanyen mai a Afirka

Najeriya ta sake komawa matsayinta ta ɗaya a cikin jerin ƙasashe masu fitar da ɗanyen mai bayan da ta samu ƙari a yawan ɗanyen man da take fitarwa a kowace rana.

A watan Mayu, alƙaluma sun sun nuna cewa Najeriya ta rinƙa fitar da ɗanyen mai ganga miliyan 1.184.

Alƙaluman wata-wata da Ƙungiyar Ƙasashe Masu Fitar da Man Fetur da Duniya (OPEC) ta fitar sun nuna cewa Najeriya ta ɗara Libya, mai fitar da ganga miliyan 1,158, da Angola mai fitar da ganga miliyan 1,111, da kuma Algeria mai fitar da ganga 962,000.

A cikin shekarar nan ta 2023 ne dai yawan ɗanyen man da Najeriya ke fitarwa zuwa ƙasashen ƙetare ya ragu matuƙa, inda ya koma ganga 999,000 a kowace rana, lamarin da ya mayar da ita bayan ƙasashen Libya da Angola da Algeria.

Najeriya dai na fama da matsalar masu satar ɗanyen mai, da rashin tsaro a yankin Neja-Delta mai arziƙin man fetur, da fasa bututan mai, waɗanda gwamnati ta ce su ne manyan dalilan da suka sanya fitar da ɗanyen man ya yi ƙasa sosai.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp