Home Labarai Gwamnatin jihar Kano ta gaggauta magance ayyukan daba a jihar – Majalisa

Gwamnatin jihar Kano ta gaggauta magance ayyukan daba a jihar – Majalisa

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta yi Kira ga Gwamnatin Jihar Kano data Umarci Kwamishinan ‘Yan sanda na Jihar da sauran hukumomin tsaro dasu Kai daukin gaggawa Unguwannin dake cikin Dala dake fuskantar matsalolin ‘Yan daba da masu kwace dake damun Yankin tsawon kwanaki.

Kiran ya biyo bayan kudurin da Shugaban Masu Rinjaye na majalisar Kuma wakilin Dala Hon Lawan Hussaini ya gabatar a zauren majalisar inda ya ce tsawon kwanaki batagari sun addabi Unguwannin na Dala da adakawa da kewaye da kwace da sare sare da tashin hankali kala kala a tsakar dare.

A cewar sa lamarin ya damu Al’ummar Yankin da tuni wasu sun fara kaura daga gidajensu saboda tsira da rayukansu kasancewar lamarin na janyo raunata mutane maza da mata..

Wakilin karamar Hukumar Rimin gado da Tofa Hon Muhammad Bello Butu-Butu da wakilin Ungoggo a majalisar Hon Aminu Saadu dana Dambatta da na Garko da Kuma na Takai cikin wadanda suka goyi bayan kudirin..

Shugaban Majalisar dokokin ta Kano Rt Hon Jibril Samaila Falgore ya bayyana amincewar Majalisar..

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp