Home Labarai Gwamnatin jihar Kano ta gaggauta magance ayyukan daba a jihar – Majalisa

Gwamnatin jihar Kano ta gaggauta magance ayyukan daba a jihar – Majalisa

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta yi Kira ga Gwamnatin Jihar Kano data Umarci Kwamishinan ‘Yan sanda na Jihar da sauran hukumomin tsaro dasu Kai daukin gaggawa Unguwannin dake cikin Dala dake fuskantar matsalolin ‘Yan daba da masu kwace dake damun Yankin tsawon kwanaki.

Kiran ya biyo bayan kudurin da Shugaban Masu Rinjaye na majalisar Kuma wakilin Dala Hon Lawan Hussaini ya gabatar a zauren majalisar inda ya ce tsawon kwanaki batagari sun addabi Unguwannin na Dala da adakawa da kewaye da kwace da sare sare da tashin hankali kala kala a tsakar dare.

A cewar sa lamarin ya damu Al’ummar Yankin da tuni wasu sun fara kaura daga gidajensu saboda tsira da rayukansu kasancewar lamarin na janyo raunata mutane maza da mata..

Wakilin karamar Hukumar Rimin gado da Tofa Hon Muhammad Bello Butu-Butu da wakilin Ungoggo a majalisar Hon Aminu Saadu dana Dambatta da na Garko da Kuma na Takai cikin wadanda suka goyi bayan kudirin..

Shugaban Majalisar dokokin ta Kano Rt Hon Jibril Samaila Falgore ya bayyana amincewar Majalisar..

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp