Home Labarai Cutar mashako ta hallaka kananan yara a jihar Kaduna

Cutar mashako ta hallaka kananan yara a jihar Kaduna

Cutar Mashaƙo ta halaka ƙananan yara uku tare da kwantar da bakwai a asibiti, bayan ɓarkewarta a ƙaramar hukumar Maƙarfi da ke jihar Kaduna.

Kamfanin dillancin labaran ƙasar NAN, ya ambato sakataren lafiya na ƙaramar hukumar Makarfi Malam Aliyu Alassan na tabbatar da haka a lokacin zantawa da shi.

Ya ce an samu ɓullar cutar a garin Tashar Na Kawu da ke mazaɓar Gubuchi a ƙaramar hukumar.

Alassan ya ce mafiya yawan waɗanda cutar ta kama ƙananan yara ne, ya ci gaba da cewa tuni aka ɗauki samfurin jininsu tare da aika shi Abuja babban birnin ƙasar domin yin gwaji don tantance cutar .

“An kai waɗanda ake zargi sun kamu da cutar zuwa asibiti, tare da killace su domin ba su kulawar da ta dace”, in ji shi.

Ma’aikatar lafiyar jihar ta tabbatar da ɓullar cutar a wasu garuruwan Kafancan da ke yankin ƙaramar hukumar Jema’a, bayan bayyanar alamomin cutar a wasu unguwanni a garin na kafancan

Cikin wata sanarwa da ya fitar gwamnan jihar Sanata Uba Sani ya umarci ma’aikatar lafiyar jihar da ta gaggauta tura tawagar likitoci zuwa garin na Kafancan domin gudanar da bincike tare da ɗaukar matakan da suka dace kan ɓullar cutar.

A baya-bayan nan cutar mashaƙo na ci gaba da ɓulla a wasu jihohin ƙasar, tare da rahotonnin rasa rayuka masu yawa a wasu jihohin.

Alamomin cutar sun haɗar da wahalar numfashi, da zazzaɓi mai zafi, da tari, da kasala, da zafin maƙogoro da kuma kumburin wuya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp