Home Labarai Cutar mashako ta hallaka kananan yara a jihar Kaduna

Cutar mashako ta hallaka kananan yara a jihar Kaduna

Cutar Mashaƙo ta halaka ƙananan yara uku tare da kwantar da bakwai a asibiti, bayan ɓarkewarta a ƙaramar hukumar Maƙarfi da ke jihar Kaduna.

Kamfanin dillancin labaran ƙasar NAN, ya ambato sakataren lafiya na ƙaramar hukumar Makarfi Malam Aliyu Alassan na tabbatar da haka a lokacin zantawa da shi.

Ya ce an samu ɓullar cutar a garin Tashar Na Kawu da ke mazaɓar Gubuchi a ƙaramar hukumar.

Alassan ya ce mafiya yawan waɗanda cutar ta kama ƙananan yara ne, ya ci gaba da cewa tuni aka ɗauki samfurin jininsu tare da aika shi Abuja babban birnin ƙasar domin yin gwaji don tantance cutar .

“An kai waɗanda ake zargi sun kamu da cutar zuwa asibiti, tare da killace su domin ba su kulawar da ta dace”, in ji shi.

Ma’aikatar lafiyar jihar ta tabbatar da ɓullar cutar a wasu garuruwan Kafancan da ke yankin ƙaramar hukumar Jema’a, bayan bayyanar alamomin cutar a wasu unguwanni a garin na kafancan

Cikin wata sanarwa da ya fitar gwamnan jihar Sanata Uba Sani ya umarci ma’aikatar lafiyar jihar da ta gaggauta tura tawagar likitoci zuwa garin na Kafancan domin gudanar da bincike tare da ɗaukar matakan da suka dace kan ɓullar cutar.

A baya-bayan nan cutar mashaƙo na ci gaba da ɓulla a wasu jihohin ƙasar, tare da rahotonnin rasa rayuka masu yawa a wasu jihohin.

Alamomin cutar sun haɗar da wahalar numfashi, da zazzaɓi mai zafi, da tari, da kasala, da zafin maƙogoro da kuma kumburin wuya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp