Home Labarai Sojojin Nijeriya sun tarwatsa maboyar mayakan IPOB a jihar Delta

Sojojin Nijeriya sun tarwatsa maboyar mayakan IPOB a jihar Delta

Rundunar sojin Najeriya tare da hadin gwiwar jami’an tsaron farin kaya sun lalata sansanin ‘yan kungiyar awaren IPOB da takwararta ta ESN a Asaba da ke jihar Delta.

Wannan na Cikin wata sanarwa da rundunar ta wallafa a shafinta na Twitter, inda ta ce jami’anta sun kaddamar da samame kan sansanin ‘yan awaren da ke tsakiyar babban dajin Asaba da safiyar ranar Asabar, inda suka samu nasarar kwato makamai.

Sojojin sun yi musayar wuta da ‘yan bindigar a lokacin samamen, inda daga bi-sani ‘yan bindigar suna gudu daga maɓoyar tasu.

Sanarwar ta ce sojojin sun kama daya daga cikin mayaƙan ‘yan awaren, tare da ƙwato bindigogi biyar kirar AK-47, da manyan bindigogi masu sarrafa kansu uku. da wata ƙirar G3 da ƙamar bindiga guda.

Sauran abubuwan da dakarun sojin suka ƙwato, sun hadar da kwanson saka alburushi biyar, da gatari da kuma tutar kungiyar IPOB.

Babban hafsan sojin ƙasa na Najeriya Manjo Janar Taoreed Lagbaja ya yaba da namijin ƙoƙarin da sojojin suka yi tare da sauran jami’an tsaro, a yunƙurinsu na kawar da ayyukan ‘yan bindigar da ke addabar yankin, tare da maido da zaman lafiya.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp