Home Labarai Sojojin Nijeriya sun tarwatsa maboyar mayakan IPOB a jihar Delta

Sojojin Nijeriya sun tarwatsa maboyar mayakan IPOB a jihar Delta

Rundunar sojin Najeriya tare da hadin gwiwar jami’an tsaron farin kaya sun lalata sansanin ‘yan kungiyar awaren IPOB da takwararta ta ESN a Asaba da ke jihar Delta.

Wannan na Cikin wata sanarwa da rundunar ta wallafa a shafinta na Twitter, inda ta ce jami’anta sun kaddamar da samame kan sansanin ‘yan awaren da ke tsakiyar babban dajin Asaba da safiyar ranar Asabar, inda suka samu nasarar kwato makamai.

Sojojin sun yi musayar wuta da ‘yan bindigar a lokacin samamen, inda daga bi-sani ‘yan bindigar suna gudu daga maɓoyar tasu.

Sanarwar ta ce sojojin sun kama daya daga cikin mayaƙan ‘yan awaren, tare da ƙwato bindigogi biyar kirar AK-47, da manyan bindigogi masu sarrafa kansu uku. da wata ƙirar G3 da ƙamar bindiga guda.

Sauran abubuwan da dakarun sojin suka ƙwato, sun hadar da kwanson saka alburushi biyar, da gatari da kuma tutar kungiyar IPOB.

Babban hafsan sojin ƙasa na Najeriya Manjo Janar Taoreed Lagbaja ya yaba da namijin ƙoƙarin da sojojin suka yi tare da sauran jami’an tsaro, a yunƙurinsu na kawar da ayyukan ‘yan bindigar da ke addabar yankin, tare da maido da zaman lafiya.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp