Home Labarai Sojojin Nijeriya sun tarwatsa maboyar mayakan IPOB a jihar Delta

Sojojin Nijeriya sun tarwatsa maboyar mayakan IPOB a jihar Delta

Rundunar sojin Najeriya tare da hadin gwiwar jami’an tsaron farin kaya sun lalata sansanin ‘yan kungiyar awaren IPOB da takwararta ta ESN a Asaba da ke jihar Delta.

Wannan na Cikin wata sanarwa da rundunar ta wallafa a shafinta na Twitter, inda ta ce jami’anta sun kaddamar da samame kan sansanin ‘yan awaren da ke tsakiyar babban dajin Asaba da safiyar ranar Asabar, inda suka samu nasarar kwato makamai.

Sojojin sun yi musayar wuta da ‘yan bindigar a lokacin samamen, inda daga bi-sani ‘yan bindigar suna gudu daga maɓoyar tasu.

Sanarwar ta ce sojojin sun kama daya daga cikin mayaƙan ‘yan awaren, tare da ƙwato bindigogi biyar kirar AK-47, da manyan bindigogi masu sarrafa kansu uku. da wata ƙirar G3 da ƙamar bindiga guda.

Sauran abubuwan da dakarun sojin suka ƙwato, sun hadar da kwanson saka alburushi biyar, da gatari da kuma tutar kungiyar IPOB.

Babban hafsan sojin ƙasa na Najeriya Manjo Janar Taoreed Lagbaja ya yaba da namijin ƙoƙarin da sojojin suka yi tare da sauran jami’an tsaro, a yunƙurinsu na kawar da ayyukan ‘yan bindigar da ke addabar yankin, tare da maido da zaman lafiya.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp