Home Labarai Babandede ya bukaci gwamnan Kano ya samar da kasuwar zamani jihar

Babandede ya bukaci gwamnan Kano ya samar da kasuwar zamani jihar

Tsohon Babban Kwantirolan hukumar kula da shige da fice na kasa Immigration, Muhammad Babandede, ya shawarci gwamnatin Kano da ta gina kasuwannin da za’ake hada-hadar kasuwanci da cinikayya na tsawon sa’o’i 24 babu yankewa, domin bunkasa tattalin arziqin jihar.

Muhammad Babandede, ya fadi hakan ne lokacin da yake gabatar da wata lakca mai taken rawar da hukumar kula da shige da fice ta kasa Immigration ke takawa wajen habaka kasuwancin jihar Kano, a wani bangare na bikin cikar hukumar shekaru 60 da kafuwa, wacce hukumar lura da shige da ficen reshan jihar Kano ta shirya a dakin taro na Labanon Club dake Unguwar Bompai.

Yace samar da kasuwannin masu ci tsawon awanni 24 a fadin jihar Kano dake zama cibiyar kasuwancin Najeriya, hakan zai taimaka matuka gaya, wajen samar da tsaro da cire da mummunan tinani a zukatan matasa da kuma bunkasa tattalin arziqin kasa da jiha baki daya.

Daga bisani Tsohon Babban Kwantirolan hukumar kula da shige da ficen na kasa Immigration, Muhammad Babandede, ya bukaci hukumar ta Immigration, reshan jihar Kano dama na sauran jihohin Najeriya da su hada hannu da sarakunan gargajiya don samun nasarar tafiyar da aiyukansu yadda yakamata.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp