Home Labarai Babandede ya bukaci gwamnan Kano ya samar da kasuwar zamani jihar

Babandede ya bukaci gwamnan Kano ya samar da kasuwar zamani jihar

Tsohon Babban Kwantirolan hukumar kula da shige da fice na kasa Immigration, Muhammad Babandede, ya shawarci gwamnatin Kano da ta gina kasuwannin da za’ake hada-hadar kasuwanci da cinikayya na tsawon sa’o’i 24 babu yankewa, domin bunkasa tattalin arziqin jihar.

Muhammad Babandede, ya fadi hakan ne lokacin da yake gabatar da wata lakca mai taken rawar da hukumar kula da shige da fice ta kasa Immigration ke takawa wajen habaka kasuwancin jihar Kano, a wani bangare na bikin cikar hukumar shekaru 60 da kafuwa, wacce hukumar lura da shige da ficen reshan jihar Kano ta shirya a dakin taro na Labanon Club dake Unguwar Bompai.

Yace samar da kasuwannin masu ci tsawon awanni 24 a fadin jihar Kano dake zama cibiyar kasuwancin Najeriya, hakan zai taimaka matuka gaya, wajen samar da tsaro da cire da mummunan tinani a zukatan matasa da kuma bunkasa tattalin arziqin kasa da jiha baki daya.

Daga bisani Tsohon Babban Kwantirolan hukumar kula da shige da ficen na kasa Immigration, Muhammad Babandede, ya bukaci hukumar ta Immigration, reshan jihar Kano dama na sauran jihohin Najeriya da su hada hannu da sarakunan gargajiya don samun nasarar tafiyar da aiyukansu yadda yakamata.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp