Home Labarai Fadar shugaban Nijeriya ta musanta batun dawo da tallafin man fetur na...

Fadar shugaban Nijeriya ta musanta batun dawo da tallafin man fetur na wucin gadi.

Babban Mai Temakawa Shugaban Ƙasa a Kan Harkokin Yaɗa Labari da Hulɗa da Jama’a. Tope Ajayi, ya ce, babu wani shirin da gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu take yi na dawo da tallafin man fetur.

Ajayi ya yi wannan bayani ne a yau Alhamis a shafinsa na X wanda a baya ake kira da Twitter da misalin ƙarfe 6:08 agogon Najeriya.

Ya rubuta cewar, babu wani shiri na dawo da duk wani Nau’I na tallafi, sannan kuma babu wani yanayi da zai sa a goyi bayan duk wani tashin farashin a wannan lokacin.
Ya ƙara da cewar, Shugaban Ƙasa Tinubu ya gamsu da cewar, bisa bayanan da yake samu, za a iya ci gaba da kasancewa kan farashin da ake kai a yanzu haka.

Wannan rubutu na Ajayi dai ya zo ne, biyo bayan labaran da suke cewa, an ɗan dawo da tallafin man fetur saboda ƙaruwar kuɗin shigo da shi wanda ya samo asali daga faɗuwar darajar naira.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp