Home Labarai Tinubu ya nada shuwagabannin NTA, VON, FRCN

Tinubu ya nada shuwagabannin NTA, VON, FRCN

Shugaban Nijeriya Bola Ahmad Tinubu ya nada Sabbin shuwagabanni hukumomi da ma’aikatun 8 dake karkashin hukumar sadarwa da wayar da kai ta kasar.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da mashawarci kan yada labarai ga shugaban kasar Ajuri Ngelale ya sanyawa hannu a birnin tarayya Abuja.

Sanarwar tace an nada: According to the statement those appointed are:

(1). Mr. Lanre Issa-Onilu matsayin shugaban hukumar wayar da kai ta (NOA)

(2) Mr. Salihu Abdulhamid Dembos matsayin shugaban gidan Talabijin na kasa  (NTA).

(3) Dr. Muhammed Bulama matsayin shugaban gidajen Radio Gwamantin Tarayya  (FRCN).

(4) Mr. Charles Ebuebu matsayin shugaban hukumar dake lura da kafafen yada labarai na Nijeriya (NBC).

(5) Mr. Jibrin Baba Ndace matsayin shugaban kafar yada labarai ta  (VON)

(6) Dr. Lekan Fadolapo shugaban hukumar dake lura da tallace-tallace a kafafen yada labarai ta (ARCON).

(7) Mr. Ali Muhammed Ali matsayin shugaban kamfanin dillancin Labarai na Nijeriya News (NAN).

(8) Mr. Dili Ezughah matsayin shugaban (NPC).

Sanarwa ta bayyana cewa Tinubu ya bukaci sabbin shuwagabannin dasu zama masu amfani da fikira wajen ciyar da inda aka dora musu nauyin lura dashi gaba, tare da jagorori na kwarai.

Ta kuma cewa nadin nasu ya fara aiki nan take.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp