Home Labarai Tinubu ya rage yawan masu yi masa rakiya

Tinubu ya rage yawan masu yi masa rakiya

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ba da sanarwar rage yawan jami’an da za su riƙa yi masa rakiya a duk tafiye-tafiyen aiki da zai je a ciki da wajen Nijeriya.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai bashi shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya sanyawa hannu kuma aka rabawa manema labarai ranar talata.

Matakin ya shafi dukkan ministoci da manyan jami’an gwamnatinsa ciki har da mataimakin shugaban ƙasa da uwargidan shugaban ƙasa.

Sanarwar ta bayyana cewa matakin, wani yunƙuri ne na rage yawan kuɗaɗen da jami’an gwamnati ke kashewa kan harkokin tafiye-tafiye.

Ta ce yawan jami’an da za su riƙa yi wa shugaban ƙasa rakiya zuwa ƙasashen waje, nan gaba ba za su wuce jami’ai 20 ba. Haka zalika, Ngelale ya ce Tinubu ya ba da umarnin a daina tura ɗumbin jami’an tsaro zuwa wata jiha a duk lokacin da zai kai ziyara can, maimakon haka za a riƙa amfani da jami’an tsaron da ke jihar ne kawai don tabbatar da tsaro.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp